An daƙile harin ‘yan ta’adda tare da ceto mutanen da aka sace

Sojojin Nijeriya sun kashe 'yan Boko Haram 16 a Borno

Sojojin rundunar Operation Hadin Kai sun kashe mayaƙan Boko Haram 16 a Jihar Borno, bayan da suka daƙile wani yunƙurin kai hari kan sansanin soji da ke Auno a ranar 5 ga Fabrairu. TRT Hausa

Wata sanarwa da kakakin rundunar, Laftanal Kanal Sani Uba, ya fitar ta ce dakarun sun yi amfani da ƙwararrun dabarun yaƙi da makamai wajen fatattakar ‘yan ta’addan da suka kai harin. TRT Hausa

Bayan haka, sojojin tare da haɗin gwiwar ‘yan sa-kai sun ƙaddamar da harin ramuwa a ranar 9 ga Fabrairu ta hanyar Komala a Ƙaramar Hukumar Konduga, inda suka kashe mayaƙa 16 a kusa da Gidan Kaji, yayin da wasu suka tsere da raunuka. TRT Hausa

Sanarwar ta ce dakarun sun ƙwace kekuna fiye da 20, makamai da wasu kayayyaki masu muhimmanci daga hannun ‘yan ta’addan. TRT Hausa

Haka kuma, sojojin sun kama wasu da ake zargi da safarar magunguna zuwa ga ISWAP a yankin Bukarti, lamarin da ya kawo cikas ga hanyoyin samar da kayayyaki ga ‘yan ta’adda. TRT Hausa

A wani bangare, dakarun sun daƙile yunƙurin garkuwa da mutane a kan hanyar Buratai zuwa Kamuye, tare da kuɓutar da Malam Idris Adamu da Malam Muhammadu Safiyanu, inda aka mayar da su ga iyalansu lafiya lau. TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#