Mai taimaka wa tsohon gwamnan kan yada labarai Muyiwa Adekeye ya wallafa a shafinsa na X cewa a ranar Alhamis cewa "A yau jami'an tsaro sun so su kama Nasir El-Rufai bayan komawarsa gida daga birnin Cairo.

Jami'an tsaro sun ƙwace fasfon Nasir El-Rufa'i bayan yunkurin kama shi ya ci tura a filin jirgi

Jami'an tsaro a babban filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe a Abuja sun ƙwace fasfon tafiye-tafiye na tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufa'i, jim kaɗan bayan saukarsa a Nijeriya daga Masar.

Mai taimaka wa tsohon gwamnan kan yada labarai Muyiwa Adekeye ya wallafa a shafinsa na X cewa a ranar Alhamis cewa "A yau jami'an tsaro sun so su kama Nasir El-Rufai bayan komawarsa gida daga birnin Cairo.

"El-Rafai ya ƙi bin su ba tare da an nuna masa takardar gayyata ba a hukumance, sai dai duk da haka sun ƙwace takardar fasfo dinsa daga hannun wani mai taimaka masa," in ji sanarwar.

Wani bidiyo da aka yi ta yaɗawa a shafukan sada zumunta ya nuna yadda Malam Nasir ke magana da wasu mutane a filin jirgin, inda yake cewa "idan kuna son ku gayyace ni ku ba ni takardar gayyata."

Lamarin na zuwa ne bayan da a ranar Laraba El-Rufai ya yi zargin cewa gwamnatin tarayya za ta iya kama shi, yana mai cewa alamu sun nuna abubuwan da ke faruwa a baya bayan nan shi ne zai zama mutum na gaba da ake hari. 

El-Rufai ya yi wannan zargi ne a yayin wata hira da DCL Hausa, yana mai nuna damuwa kan abin da ya bayyana a matsayin ƙaruwar barazanar siyasa ga abokan hamayya.

Tsohon gwamnan na Kaduna wanda ya bar APC mai mulki zuwa ADC ya ce tuni an kama wasu abokan hulɗarsa an tsare.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#