Matakin na nufin ƙarfafa haɗin gwiwar soji tsakanin Abuja da Washington

Amurka za ta tura dakaru 200 Nijeriya domin horas da sojoji

Amurka ta sanar da shirin tura dakaru 200 zuwa Nijeriya domin horas da dakarun sojin ƙasar a yaƙinsu da ƙungiyoyin ‘yan ta’adda, kamar yadda jami’an Nijeriya da na Amurka suka bayyana ranar Talata. TRT Hausa

Matakin na zuwa ne yayin da Amurka ke ƙara ƙulla alaƙa ta soji da ƙasar Yammacin Afirka, inda Manjo Janar Samaila Uba, mai magana da yawun rundunar tsaron Nijeriya, ya ce sojojin Amurka za su taimaka wajen horaswa da kuma ba da tallafin fasaha. TRT Hausa

Rahotanni sun ce dakarun za su yi aiki tare da wata ƙaramar tawagar sojojin Amurka da ke Nijeriya, domin taimaka wa ƙasar wajen kai hare-hare ta sama kan ‘yan ta’adda, tare da bayar da horo da shawarwarin fasaha kan haɗa ayyukan soji na sama da ƙasa. TRT Hausa

Mai magana da yawun rundunar sojin Afirka ta Amurka ya tabbatar da shirin, yayin da Nijeriya ke fuskantar matsin lamba daga Washington kan matsalar rashin tsaro, duk da cewa Abuja ta yi watsi da zargin cewa ana kai wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar. TRT Hausa

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#