Kwastam na ƙasashen biyu sun amince da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauƙaƙa zirga-zirgar kayayyaki

Nijeriya da Nijar sun ƙulla yarjejeniya kan tsaron iyaka da kasuwanci

Hukumar Kwastam ta Nijeriya da Gwamnatin Jamhuriyar Nijar sun cimma yarjejeniya ta dabarun haɗin gwiwa kan tsaron iyaka, kare kayayyakin da ke wucewa ta iyakoki da kuma bunƙasa hulɗar tattalin arziƙi tsakanin ƙasashen biyu. TRT Hausa

Babban Kwanturola Janar na Kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi, ya bayyana hakan ne a wani taron tattaunawar haɗin gwiwa da aka gudanar a Abuja, inda tawagar Kwastam ta Nijar ke ƙarƙashin jagorancin Darakta Janar, Muhammadu Yaqouba. TRT Hausa

Adeniyi ya ce haɗin gwiwar za ta mayar da hankali kan sauƙaƙa kasuwancin yankin, kare kayayyakin da ke wucewa, musayar bayanai da kuma inganta tsaro a kan iyakokin ƙasashen biyu. TRT Hausa

Ya bayyana cewa an tsara yarjejeniyar ne domin inganta jigilar kayayyaki zuwa Nijar ta hanyar Nijeriya, rage jinkiri a hanyoyin wucewa da kuma magance matsalolin tsaro, domin kasuwanci na halal ya taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙin ƙasashen biyu. TRT Hausa

Babban Kwanturola Janar ɗin ya amince cewa ƙasashen da ba su da tashar ruwa na fuskantar ƙalubale, yana mai jaddada cewa Nijeriya za ta ci gaba da tallafa wa Nijar da sauran maƙwabta wajen sauƙaƙa kasuwanci, duk da bambance-bambancen siyasa. TRT Hausa

Ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya amince da kafa hanyoyin tsaro na musamman da izinin wucewa cikin aminci domin sauƙaƙa zirga-zirgar manyan motocin kaya a kan iyakoki. TRT Hausa

 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#