An dasa bam ɗin ne a hanyar Danjibga zuwa Kuncin Kalgo a Tsafe

Jami’an tsaro sun kwance bam a hanyar Zamfara

Jami’an tsaron Nijeriya sun samu nasarar kwance wani bam da ake zargin ‘yan ta’adda ne suka dasa a kan hanyar Danjibga zuwa Kuncin Kalgo a Ƙaramar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara. TRT Hausa

Aikin kwance bam ɗin ya gudana ne ta haɗin gwiwar rundunar kwance bama-bamai ta ‘yansandan Nijeriya, Sashen Yaƙi da Garkuwa da Mutane, da rundunar EOD ta Sojoji, tare da cikakken tsaro daga rundunar ‘yansandan jihar. TRT Hausa

Kakakin rundunar ‘yansandan Zamfara, Yazid Abubakar, ya ce SP Abdulrazak Musa Hassan ne ya jagoranci aikin, inda jami’an suka yi amfani da dabarun ƙwarewa wajen kwance sassan bam ɗin da aka adana domin binciken kimiyya. TRT Hausa

Bayan cikakken bincike a yankin, hukumomin tsaro sun ayyana hanyar a matsayin mai aminci, lamarin da ya dawo da kwanciyar hankali ga masu ababen hawa da mazauna yankin. TRT Hausa

Hukumomin sun buƙaci al’umma su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai cikin gaggawa, yayin da ake ci gaba da fuskantar barazanar hare-haren ‘yanbindiga a jihohin arewa maso yammacin Nijeriya. TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#