Sport
Fadar ta ce za a tarbi Shugaba Tinubu da matarsa, Oluremi Tinubu, a Fadar Windsor, a yammacin London, inda Sarki Charles da Sarauniya Camilla za su tarbe su.
Sarkin Charles na uku na Birtaniya zai karɓi baƙuncin Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, a wata ziyara ta ƙasa da ƙasa da zai kai ta yini biyu zuwa Birtaniya a ranakun 18–19 ga Maris, in ji Fadar Buckingham a wani bayani a ranar Asabar.
Fadar ta ce za a tarbi Shugaba Tinubu da matarsa, Oluremi Tinubu, a Fadar Windsor, a yammacin London, inda Sarki Charles da Sarauniya Camilla za su tarbe su.
London da Abuja sun kulla wani kawance ta dabaru a watan Nuwamban 2024 don ƙarfafa haɗin kansu kan harkokin tattalin arziki, shige da fice, da tsaro.
Nijeriya wadda ke yammacin Afirka na fama da ta'addanci tsawon shekaru a arewa maso gabas, da kuma garkuwa da mutane don neman kuɗin fansa daga ƙungiyoyin ta’addanci a arewa maso yamma da tsakiyar ƙasar.
A ranar Juma'a, Ma'aikatar Tsaron Nijeriya ta ce ƙasashen biyu suna shirin ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro jim kaɗan bayan kisan mutane fiye da 160 a Jihar Kwara da ke tsakiyar ƙasar wanda Shugaba Tinubu ya danganta ga 'yan ta'adda.
Azabtarwar mulkin mallaka
Nijeriya ƙasa ce wadda Birtaniya ta yi wa mulkin mallaka kuma mamba ce ta ƙasashen renon Ingila inda take da aƙalla mutum miliyan 230, kuma tana daga cikin manyan tattalin arzikin nahiyar.
Ko da yake Charles ya tarbi Shugaba Tinubu a watan Satumban 2024, wannan tafiya za ta kasance ziyarar ƙasa ta farko a hukumance daga shugaban Nijeriya zuwa Burtaniya cikin shekaru 37.
Charles ya ziyarci Nijeriya sau huɗu a lokacin da yake Yarima na Wales kafin rasuwar mahaifiyarsa, Sarauniya Elizabeth II, a 2022.
A ranar Juma'a, kotun Nijeriya ta umarci gwamnatin Birtaniya da ta biya fam £420 miliyan ga iyalan masu haƙar ma'adinan da aka kashe a 1949 ta hannun masu mulkin mallaka, bayan da suka yi zanga-zangar yanayin aikin su da albashin da ba a biya su ba ta hanyar mamaye ma'adinan da suke aiki a ciki.
Wannan kisan dai yana cikin jerin azabtarwar da Birtaniya ta aikata a lokacin mulkin mallaka a Nijeriya da sauran sassan Afirka.
Comments
No comments Yet
Comment