Nijeriya na shirin cin gajiyar kasuwar halal ta duniya mai darajar dala tiriliyan 7.7

Tinubu ya ƙaddamar da Tsarin Tattalin Arzikin Halal na Ƙasa

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ƙaddamar da Tsarin Tattalin Arzikin Halal na Ƙasa domin bai wa ƙasar damar cin gajiyar kasuwar halal ta duniya wadda aka ƙiyasta darajarta ta kai dala tiriliyan 7.7, tare da faɗaɗa tattalin arzikin Nijeriya. TRT Hausa

Tinubu, ta bakin Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, ya ce shirin na nuna aniyar Nijeriya ta shiga kasuwar halal ta duniya, inda ake sa ran zai ƙara kusan dala biliyan 1.5 ga tattalin arzikin ƙasar nan da shekarar 2027. TRT Hausa

Tsarin zai mayar da hankali kan faɗaɗa fitar da abinci mai bin ƙa’idar halal, bunƙasa masana’antar magunguna da kayan kwalliya, inganta yawon buɗe ido na halal, da samar da hanyoyin kuɗi masu ɗa’a, tare da hasashen samar da darajar tattalin arziki da ta haura dala biliyan 12 nan da 2030. TRT Hausa

Gwamnatin Tarayya ta ce tattalin arzikin halal ba addini kaɗai ba ne, illa kasuwa ta duniya da ke mai da hankali kan inganci da tsaro, tare da taimakawa manufofin jawo jarin waje, faɗaɗa fitar da kayayyaki, da samar da ayyukan yi masu ɗorewa. TRT Hausa

 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#