Hukumomin sun ce lalata fibre-optic laifi ne kuma na iya kaiwa ga hukunci a kotu

NCC da NSCDC sun gargadi kamfanonin gine-gine kan lalata layukan sadarwa

Hukumar Kula da Sadarwa ta Nijeriya (NCC) da Hukumar Kare Farar-Hula ta Nijeriya (NSCDC) sun gargadi kamfanonin gine-gine da masu ayyukan injiniya da su daina lalata layukan sadarwa na fibre-optic da ke ƙarƙashin ƙasa yayin gyaran hanyoyi da sauran ayyukan gine-gine. TRT Hausa

Hukumomin sun bayyana cewa lalata layukan sadarwa ba za a ƙara lamunta ba, suna mai jaddada cewa yawancin lalacewar na faruwa ne sakamakon sakaci, kuma hakan laifi ne da zai iya kai wa ga gurfanarwa a kotu. TRT Hausa

A cikin wata sanarwar haɗin gwiwa, NCC da NSCDC sun bayyana layukan fibre-optic a matsayin muhimman kadarorin ƙasa da ke tallafa wa tattalin arzikin zamani, harkokin kasuwanci, da kuma sadarwar gwamnati a Nijeriya. TRT Hausa

Sun yi gargaɗin cewa lalata irin waɗannan kayayyakin more rayuwa na iya jefa tsaron ƙasa, tattalin arziki da lafiyar jama’a cikin haɗari. TRT Hausa

Hukumomin sun ƙara da cewa a ƙarƙashin Dokar Kare Muhimman Kayayyakin Sadarwa na Ƙasa (CNII Order 2024), an ayyana layukan fibre-optic a matsayin muhimman kayayyakin sadarwa na ƙasar. TRT Hausa

Sun bayyana cewa duk wanda ya lalata layukan ta hanyar haƙar ƙasa, aikin gini ko rashin tuntuba da hukumomin da abin ya shafa—ko mutum ɗaya ne, kamfani ko ɗan kwangilar gwamnati—zai fuskanci hukunci da sauran matakan doka kamar yadda dokoki suka tanada. TRT Hausa

 
 
 
 
 

 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#