Harin a jihar Kwara ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 170

Benin da AU sun yi Allah wadai da harin ta’addanci a Nijeriya

Jamhuriyar Benin da Tarayyar Afirka (AU) sun bayyana ta’aziyyarsu tare da yin Allah wadai da wani harin ta’addanci da aka kai a Nijeriya, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 170, kamar yadda aka bayyana a ranar Alhamis. TRT Hausa

Gwamnatin Benin ta miƙa “ta’aziyya ta musamman” ga iyalan waɗanda abin ya shafa, al’ummar Nijeriya da gwamnati, tare da sake jaddada goyon bayanta ga ƙoƙarin Abuja na yaƙi da ta’addanci da tsattsauran ra’ayi a yankin. TRT Hausa

Shugaban Hukumar AU, Mahmoud Ali Youssouf, ya bayyana harin a matsayin mummunan aiki da rashin imani, yana mai cewa babban take haƙƙin ɗan’adam ne kuma barazana ga zaman lafiya da tsaro, kamar yadda sanarwar AU ta bayyana. TRT Hausa

Youssouf ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu tare da tabbatar da cikakken goyon bayan AU ga gwamnatin Nijeriya da hukumomin Jihar Kwara. TRT Hausa

Gwamnatin Jihar Kwara ta ce an riga an binne mutum 75 a kabarin bai-ɗaya, yayin da wani ɗan majalisa ya bayyana cewa an gano gawawwaki 170, kuma ana sa ran adadin zai ƙaru yayin da ake ci gaba da bincike. TRT Hausa

Jihar Kwara dai na fuskantar ƙarin matsalolin tsaro a ‘yan watannin nan, musamman a yankunan da ke kusa da dazuzzuka, sakamakon hare-haren ‘yan fashi da makami, garkuwa da mutane da kuma matsin lambar soji a jihohin maƙwabta. TRT Hausa

 
 
 
 
 
#