Publication : 6 February 2026
Update : 6 February 2026
Harin a jihar Kwara ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 170
Jamhuriyar Benin da Tarayyar Afirka (AU) sun bayyana ta’aziyyarsu tare da yin Allah wadai da wani harin ta’addanci da aka kai a Nijeriya, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 170, kamar yadda aka bayyana a ranar Alhamis. TRT Hausa
Gwamnatin Benin ta miƙa “ta’aziyya ta musamman” ga iyalan waɗanda abin ya shafa, al’ummar Nijeriya da gwamnati, tare da sake jaddada goyon bayanta ga ƙoƙarin Abuja na yaƙi da ta’addanci da tsattsauran ra’ayi a yankin. TRT Hausa
Shugaban Hukumar AU, Mahmoud Ali Youssouf, ya bayyana harin a matsayin mummunan aiki da rashin imani, yana mai cewa babban take haƙƙin ɗan’adam ne kuma barazana ga zaman lafiya da tsaro, kamar yadda sanarwar AU ta bayyana. TRT Hausa
Youssouf ya miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasa rayukansu tare da tabbatar da cikakken goyon bayan AU ga gwamnatin Nijeriya da hukumomin Jihar Kwara. TRT Hausa
Gwamnatin Jihar Kwara ta ce an riga an binne mutum 75 a kabarin bai-ɗaya, yayin da wani ɗan majalisa ya bayyana cewa an gano gawawwaki 170, kuma ana sa ran adadin zai ƙaru yayin da ake ci gaba da bincike. TRT Hausa
Jihar Kwara dai na fuskantar ƙarin matsalolin tsaro a ‘yan watannin nan, musamman a yankunan da ke kusa da dazuzzuka, sakamakon hare-haren ‘yan fashi da makami, garkuwa da mutane da kuma matsin lambar soji a jihohin maƙwabta. TRT Hausa
Migration: South Africa to relocate refugee centres to border entry points
President Cyril Ramaphosa says South Africa cannot tackle migration challenges alone, and has called for greater cooperation across the continent.
Davido, Burna Boy, Rema and Tyla set for 2026 World Cup
Davido has been selected to headline the official FIFA World Cup Countdown Concert on 10 June, 2026 in Los Angeles, United States.
Mauritius rejects reported US proposal to purchase Chagos Islands
Mauritius maintains its its sovereignty over the Chagos Islands is non-negotiable.
Most Read
All rights reserved. Newstimetr © 2023