Tarayyar Afirka ta ce harin "abin ban tsoro da rashin imani" ne; yayin da ita ma Jamhuriyar Benin ta mika ta'aziyya ga Nijeriya.

Jamhuriyar Benin da AU sun yi Allah wadai da harin ta'addanci da ya kashe mutum 170 a Nijeriya

Jamhuriyar Benin da Tarayyar Afirka (AU) sun bayyana ta'aziyyarsu a ranar Alhamis tare da yin Allah wadai da wani harin ta'addanci da aka kai a Nijeriya, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum 170.

Jamhuriyar Benin ta bayyana "ta'aziyyarta ta musamman" ga iyalan wadanda abin ya shafa, al'ummar Nijeriya da kuma gwamnati.

Ta sake jaddada goyon bayanta ga Abuja wajen yaki da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi, inda ta nuna muhimmancin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

Shugaban Hukumar AU Mahmoud Ali Youssouf ya kira harin a matsayin "mummunan aiki da rashin imani," wani mummunan take hakkin dan’adam da kuma wani hari "wanda ba za a yarda da shi ba" kan zaman lafiya da tsaro, a cewar wata sanarwa da aka fitar ranar Laraba.

Youssouf ya mika ta'aziyya ga iyalan wadanda abin ya shafa tare da bayyana "cikakken goyon baya" ga gwamnatin Nijeriya da hukumomin Jihar Kwara.

Ƙungiyar AU ta sake jaddada ƙudirinta na tallafa wa ƙoƙarin Nijeriya na ƙarfafa zaman lafiya, tsaro da kwanciyar hankali a faɗin ƙasar.

Gwamnatin Jihar Kwara ta tabbatar da cewa an binne mutum 75 a kabarin bai-ɗaya ranar Laraba, amma ɗan majalisar yankin Saidu Baba Ahmed ya shaida wa Anadolu a ranar Alhamis cewa an gano gawawwaki 170, kuma ana sa ran adadin wadanda suka mutu zai ƙaru.

"Bayanan da ke hannuna sun nuna cewa adadin wadanda suka mutu ya kai 170. Don haka, mutanenmu har yanzu suna cikin daji suna neman karin gawawwaki. An sace mata 35. Wadanda suka tsira su ma suna neman mafaka a cikin daji," in ji shi.

Jihar Kwara, musamman al'ummomin da ke maƙwabtaka da dazuzzuka, a cikin 'yan watannin nan ta fuskanci ƙalubalen tsaro da ke ƙaruwa mai alaƙa da fashi da makami, garkuwa da mutane da kuma ƙungiyoyi masu dauke da makamai da ke tserewa daga matsin lambar soja a jihohin da ke maƙwabtaka da ita a yankunan arewa maso yamma da arewa maso tsakiya.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#