Sport
Dollar
41,3085
-0.13 %Euro
48,5978
0.03 %Gram Gold
4.835,6300
-0.21 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Mahmud Usman ya amsa laifin haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba inda yake amfani da kuɗinsu wajen sayen makamai domin kai hare-haren ta’addanci da yin garkuwa da mutane.
Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta samu Mahmud Usman, ɗaya daga cikin kwamandojin Ansaru, wata ƙungiyar ta’addancin da aka haramta, da laifi tare da yi masa ɗaurin shekara 15.
Usman, wanda aka fi sani da suna Abu Barra, hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta gurfanar da shi a gaban kotu, kuma ya amsa laifin haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.
Laifukan da suka saɓa wa doka su suka ba shi damar sayen makamai domin ta’addanci da garkuwa da mutane, in ji takardar tuhumar da aka yi masa.
Sai dai alƙalin kotun, Maishari’a Emeka Nwite, ya ba da umarnin a ci gaba da tsare shi a hannun DSS har zuwa lokacin da za a yi masa shari’a kan sauran tuhume-tuhume 31 da hukumar ta yi masa.
A cikin takardar ƙara mai tuhume-tuhume 32 da DSS ta gabatar a gaban babbar kotun gwamnatin tarayyar, an tuhumi Usman da Abubakar Abba da aikata ayyukan ta’addanci a shekarar 2022 ta hanyar kai hari kan barikin Wawa Cantonment na sojin Nijeriya a Kainji, New Bussa, da ke ƙaramar hukumar Borgu ta Jihar Neja.
An kuma yi zargin cewa sun samu horo kan amfani da makamai da kuma haɗa bamabamai a sansanonin ‘yan ta’adda.
Kazalika an tuhume su da samun horo kan dabarun yaƙi daga wata ƙungiyar ta’addanci a ƙasar Mali.
Bayan ɗaurin na shekara 15, Mai shari’a Nwite ya saka ranar 21 ga watan Oktoba a matsayin ranar shari’ar sauran tuhume-tuhume da ake yi masa.
Hukumar DSS ta zargi kwamandodin kan kitsa harin watan Yulin shekarar 2022 a gidan yarin Kuje da ke Abuja inda suka kuɓutar da fursunoni 600.
Comments
No comments Yet
Comment