Dollar

41,3081

0.07 %

Euro

49,0017

0.41 %

Gram Gold

4.871,7500

0.3 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Bayanin ministan na zuwa ne bayan 'yan majalisar dokokin Ghana na jam'iyyu marasa rinjaye sun soki matakin gwamnati na karɓar mutum 14 da aka kora daga Amurka ba tare da neman izinin majalisa ba.

Ghana za ta karɓi ƙarin mutum 40 da za a kora daga Amurka

Ministan harkokin wajen Ghana, Samuel Okudzeto Ablakwa, ya bayyana cewa ƙasar za ta karɓi ƙarin mutum 40 da za a kora daga Amurka a kwanaki kaɗan masu zuwa.

Bayanin ministan na zuwa ne bayan 'yan majalisar dokokin Ghana na jam'iyyu marasa rinjaye sun soki matakin gwamnati na karɓar mutum 14 da aka kora daga Amurka ba tare da neman izinin majalisa ba.

Sai dai kuma gwamnati ta bayyana cewa shirin karɓar mutanen an yi shi bisa yarjejeniyar fahimtar juna da ƙasar ta ƙulla da Amurka, wadda ba ta buƙatar amincewar majalisa.

Da yake magana a wani shiri na gidan talabijin ɗin Channel One ranar Laraba, Ablakwa ya tabbatar da cewa wani sabon rukuni na mutanen da aka kora daga Amurka zai isa ƙasar Ghana nan ba da jimawa ba.

“Zan iya bayyana muka cewa muna sa rai ƙarin mutum 40 za su iso Ghana nan da kwanaki kaɗan masu zuwa. Mun tantance su kafin su zo,” in ji shi.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#