Dollar

41,2736

-0.05 %

Euro

49,0197

0.81 %

Gram Gold

4.895,1000

0.21 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Hadin kan ya zama wani mataki mai matukar muhimmanci a fannin karfafa hadin gwiwa a fannin ilimi tsakanin Nijeriya da Somalia.

Jami’ar ABU da ke Nijeriya ta yi bikin yaye daliban likitanci na Somalia masu sanin makamar aiki

Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria ta gudanar da taron bankwana don murnar kammala sanin makamar aiki na shekara guda da daliban likitanci ‘yan kasar Somalia su 23 suka yi a jami’ar.

Shugaban Jami’ar, Farfesa Adamu Ahmed ne ya jagoranci bikin da aka gudanar a Babban Dakin Taron Sanatocin Jami’ar.

Taron ya samu halartar Mai Girma Jamal Barrow, Jakadan Somalia a Nijeriya, wanda shi ne Babban Bako na Musamman.

Wadannan ne rukuni na farko na daliban likitanci na Somalia da aka horar a kwalejin aikin likitanci ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria, bayan Yarjejeniyar Fahimtar Juna da aka sanya hannu a kai tsakanin ABU da Jami’ar SIMAD ta Mogadishu a watan Fabrairun 2024.

Da yake jawabi a wajen taron, Jakada Barrow ya bayyana bikin yaye daliban a matsayin lokaci na alfahari da Somalia da Nijeriya, yana mai nuna muhimmancin hadin kai a fannin ilimi a matsayin babban jigon alakar kasashen biyu.

“Baya ga yarjeniyoyin siyasa da musayar diflomasiyya, mutane ne ke gina gada mafi karfi a tsakanin kasashe - musamman ma matasa - da suke musayar ilimi, al’adu da kwarewar rayuwa,” in ji shi.

Ya yi tsokaci da cewa daliban da suka samu horon ba ilimin likitanci kawai suka samu ba, har da ma koyon al’adu da jin su ma na Nijeriya ne, wanda hakan zai karfafa musu wajen inganta kula da lafiya a Somalia.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#