Dollar

41,3970

0.08 %

Euro

48,6749

-0.05 %

Gram Gold

4.844,4300

0.33 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Wannan na zuwa ne bayan wata sanarwar haɗin gwiwa da Masar da Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa, da Amurka suka fitar inda suka yi kira da tsagaita wuta domin barin kayan agaji shiga sassan Sudan.

Sudan ta yi maraba da ƙoƙarin kawo ƙarshen yaƙi da RSF, ta yi watsi da katsalandan na ƙasashen waje

Sudan ta yi maraba da kokarin kawo ƙarshen yaƙin da ake yi a ƙasar da kuma hare-haren da dakarun Rapid Support Forces (RSF) ke kaiwa, tana mai jaddada kin amincewa da duk wani shisshigi daga ƙasashen waje cikin harkokin cikin gida na ƙasar.

“Gwamnatin Sudan tana maraba da duk wani yunƙuri na yankin ko na ƙasa da ƙasa da zai taimaka wajen kawo ƙarshen yaƙin, dakatar da hare-haren ta’addanci na dakarun RSF kan birane da kayayyakin more rayuwa, da kuma cire takunkumin da aka sanya wa birane domin kada a sake maimaita bala’o’i da laifukan da aka aikata wa al’ummar Sudan,” in ji Ma’aikatar Harkokin Waje a wata sanarwa da ta wallafa a X ranar Asabar.

Sanarwar ta biyo bayan wata sanarwar haɗin gwiwa daga Masar, Saudiyya, Hadaddiyar Daular Larabawa, da Amurka, inda suka buƙaci a samu “tsagaita wuta ta jin kai” a Sudan domin ba da damar shigar kayan agaji cikin sauri zuwa dukkan sassan ƙasar.

Fadan El-Fasher

Ma’aikatar ta sake jaddada kin amincewa da duk wani “shisshigi na ƙasa da ƙasa ko na yankin da ba ya mutunta ikon mulkin Sudan, cibiyoyin ta na doka, da kuma hakkinta na kare mutanenta da kasarta.”

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#