Hukumomi sun danganta lamarin da ‘yan tawayen M23 a South Kivu

An Gano Manyan Ƙaburbura 170 a Gabashin DR Congo

Hukumomi da wata ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama sun ce an gano manyan ƙaburbura biyu ɗauke da gawarwaki 170 a gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo, a wani yanki da ƙungiyar ‘yan tawayen M23 ta bari kwanan nan.

Gwamnan lardin South Kivu, Jacques Purusi, ya ce an gano kaburburan a unguwannin Kiromoni da Kavimvira a wajen birnin Uvira. Ya bayyana cewa an gano kabari ɗaya mai ɗauke da kimanin gawarwaki 30 a Kiromoni, kusa da iyakar Burundi, yayin da a Kavimvira aka gano gawarwaki 141.

Ƙungiyar Local Network for the Protection of Civilians ta ce ta nemi zuwa wuraren, amma sojojin gwamnati sun hana ta. Mataimakin shugabanta, Yves Ramadhani, ya ce bayanan farko sun nuna cewa M23 ne ke da alhakin kashe mutanen, bisa zargin cewa suna zaton sojojin gwamnati ne ko mayaƙan da ke goyon bayanta.

Rikici a gabashin DR Congo ya ƙara ƙamari duk da yarjejeniyar zaman lafiya da Amurka ta jagoranta domin rage tashin hankali. Sojojin gwamnati da M23 duka sun fuskanci zarge-zargen kisan gilla da cin zarafin bil’adama daga ƙungiyoyin kare haƙƙi.

Gano kaburburan na zuwa ne yayin da rikicin ke ci gaba da raba fararen hula da muhallansu tare da zurfafa matsalar tsaro a yankin.

Tushen labari: TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#