Sport
Dollar
40,3813
0.21 %Euro
47,1097
0.62 %Gram Gold
4.355,7200
0.67 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Kiyawa, ya tabbatar da kama ɗaliban, inda ya ce ana gudanar da bincike don tantance irin rawar da kowane ɗalibi ya taka a cikin lamarin.
Rundunar ‘yan sandan Nijeriya reshen Jihar Kano ta tabbatar da cafke ɗalibai 11 na makarantar makarantar sakandare ta kwana da ke Bichi bisa zargin kisan gillan da aka yi wa wasu ɗalibai biyu.
An bayyana sunayen waɗanda aka kashe da Hamza Idris Tofawa da Umar Yusuf Dungurawa, waɗanda aka ce abokan karatunsu ne suka kai musu hari da wasu ƙarafa masu kaifi da ake kira “Gwale-Gwale.”
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Kano, Abdullahi Kiyawa, ya tabbatar da kama ɗaliban, inda ya ce ana gudanar da bincike don tantance irin rawar da kowane ɗalibi ya taka a cikin lamarin.
“An kama dalibai 11 dangane da wannan lamari, kuma ana ci gaba da bincike don gano yadda kowane ɗalibi ya taka rawa,” in ji Kiyawa a wata saƙo da ya aika wa Channels Television.
Kiyawa ya tabbatar da cewa rundunar ta za ta ƙara bayar da himma wajen ganin an tabbatar da adalci ga waɗanda abin ya shafa da iyalansu.
Comments
No comments Yet
Comment