Adadin ya ƙaru da kashi 22% yayin da ake zargin sauya matsayar wurin mai tsarki

Rahoto: Sama da ‘Yan-kama-wuri-zauna 65,000 Sun Shiga Harabar Masallacin Ƙudus a 2025

Fiye da Yahudawa ‘yan-kama-wuri-zauna 65,000 ne suka shiga harabar Masallacin Ƙudus da ke Gabashin Birnin Ƙudus a shekarar 2025, a cewar wani rahoton shekara-shekara da Gidauniyar Birnin Ƙudus ta ƙasa da ƙasa ta fitar, bisa ƙididdigar kwamitin Waqf na Musulunci.

Rahoton ya ce mutum 65,364 sun shiga wurin cikin shekara guda, ƙarin kashi 22 cikin 100 idan aka kwatanta da 2024. Haka kuma, ziyara masu alaƙa da ‘yan siyasar Isra’ila sun ƙaru daga tara zuwa 20 a cikin shekarar.

Rahoton ya ambaci Ministan Tsaron Cikin Gida na Isra’ila, Itamar Ben-Gvir, a cikin ‘yan siyasar da suka shiga harabar tare da wasu ‘yan majalisa.

An kuma ce hukumomin Isra’ila sun ɗauki sabbin matakai da suka haɗa da tsawaita awannin ziyara da ƙara adadin masu shiga daga mutum 120 zuwa 200 a rukuni guda, abin da aka bayyana a matsayin ƙoƙarin sauya daɗaɗɗiyar matsayar wurin mai tsarki.

Baya ga haka, rahoton ya ce manufofin ƙwace takardun zama sun ci gaba, inda Falasɗinawa 14,929 suka rasa katin shaidarsu tsakanin 1967 da 2024. Haka kuma, an bayyana ƙarancin ajujuwa kimanin 1,500 a Gabashin Birnin Ƙudus, tare da cewa kashi 27 cikin 100 na ɗaliban Falasɗinawa masu shekaru 6 zuwa 17 suna karatu a manhajar Isra’ila.

Gidauniyar ta yi gargaɗin cewa ana fuskantar wani sabon salo na sauyi a birnin, yayin da bayanan Isra’ila suka nuna adadi mafi girma, inda suka ce Yahudawa masu ziyara 76,448 ne suka shiga harabar a 2025, ƙarin kashi 31 cikin 100 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

Tushen labari: TRT Hausa

 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#