Sport
- Sport
- World
- Insight
- Africa
- Business
- Life
- Opinion
- Staff Reporter
- Business & Technology
- Pauline Odhiambo
- Politics
- Charles Mgbolu
- Arts & Culture
- War On Gaza
- Business & Technology
- Guinness World Record For The Longest Chess
- Cryptocurrency Trading Platform
- Arts & Culture
- Sylvia Chebet
- The Record Attempt Kicked Off On April 17th
- Despite Efforts To Stop The Killings.
- Emmanuel Oduor
- Climate Change
- Semblance Of Security Returns
- Medicinal Plants
- Firmain Eric Mbadinga
- Kategori bulunamadı
- Nuri Aden
- Burna Boy Has Worked To Carve A Unique Space For Himself
- Dayo Yussuf
- Edward Qorro
- Sudan Begins Rebuild Of Khartoum Amid Devastating Civil War
- Chess Federation
- Millicent Akeyo
- From Onana To Kudus: African Stars Missing At Afcon
- Egypt Recorded 19 Million Tourists In 2025: Minister
- Brian Okoth
- Died At The Age Of 54
Sun ce ayyana yankuna a matsayin “filin ƙasa” ya karya dokokin ƙasa da ƙasa
Ministocin harkokin wajen Turkiyya, Masar, Jordan, Indonesia, Pakistan, Qatar, Saudi Arabia da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa sun fitar da sanarwar haɗin gwiwa a ranar Talata suna Allah wadai da matakin Isra’ila na ayyana manyan yankuna a Gaɓar Yamma da aka mamaye a matsayin “filin ƙasa”, suna mai kiran matakin babban wuce-gona-da-iri.
TRT Hausa
A cewar sanarwar da Ma’aikatar Harkokin Wajen Turkiyya ta fitar, ministocin sun soki amincewar Isra’ila da shirin yin rijista da daidaita mallakar filaye a yankuna da dama na Gaɓar Yamma da aka mamaye, suna cewa matakin haramun ne kuma zai hanzarta faɗaɗa matsugunan ‘yan kama wuri zauna da ƙwace filayen Falasɗinawa.
TRT Hausa
Ministocin sun bayyana cewa matakin ya saba wa dokokin jinƙai na ƙasa da ƙasa, ciki har da Yarjejeniyar Geneva ta Huɗu, da kuma ƙudurorin Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, musamman Ƙuduri na 2334 wanda ke buƙatar Isra’ila ta dakatar da faɗaɗa matsugunai.
TRT Hausa
Sanarwar ta kuma yi nuni da ra’ayin Kotun Duniya (ICJ), inda ta ce duk wasu matakai da ke sauya matsayin shari’a, tarihi da na al’umma na yankunan Falasɗinu da aka mamaye haramtattu ne a ƙarƙashin dokokin ƙasa da ƙasa.
TRT Hausa
Ministocin sun yi gargaɗin cewa matakin Isra’ila na iya kawo sabon tsarin shari’a da gudanarwa wanda ke barazana ga mafitar ƙasashe biyu, tare da ƙara tayar da hankula a yankin. Sun kuma yi kira ga al’ummar duniya da su ɗauki matakai masu ƙarfi don kare haƙƙin Falasɗinu da tabbatar da kafa ƙasa mai ‘yanci a kan iyakokin 4 ga Yunin 1967 tare da Gabashin Kudus a matsayin babban birninta.
TRT Hausa
Comments
No comments Yet
Gabas Ta Tsakiya
Corbyn Ya Bayyana Rahoton Gawarwaki Masu Tayarda Hankali Daga Gaza
- 24 February 2026
- 5 Views
OIC za ta kira taron gaggawa kan Gabar Yamma
- 23 February 2026
- 3 Views
Saudiyya Ta Tabbatar Da Ganin Jinjirin Ramadan
- 18 February 2026
- 15 Views
Trump na duba yiwuwar tura karin jiragen yaƙi kusa da Iran
- 12 February 2026
- 6 Views
Latest News
Cameroon says arrested opposition figure Anicet Ekane died of 'natural' causes
- 25 February 2026
- 2 Views
Cameroon says arrested opposition figure Anicet Ekane died of 'natural' causes
- 25 February 2026
- 3 Views
Cameroon says arrested opposition figure Anicet Ekane died of 'natural' causes
- 24 February 2026
- 5 Views
Cameroon says arrested opposition figure Anicet Ekane died of 'natural' causes
- 24 February 2026
- 5 Views
Comment