Hatsarin ya faru ne a arewacin ƙasar yayin tsallaka kogin.

Kwale-kwale Ya Nutse a Kogin Nilu, Mutum 21 Sun Mutu a Sudan

Aƙalla mutum 21 sun mutu bayan wani kwale-kwale ya nutse a Kogin Nilu a arewacin Sudan, kamar yadda gwamnatin jihar da ganau suka bayyana.
TRT Hausa

Gwamnatin Jihar River Nile ta ce an gano gawarwaki 21 tare da bayyana sunayensu, yayin da ta gargaɗi cewa har yanzu ba a san inda wasu daga cikin fasinjojin suke ba, a cewar rahoton kamfanin dillancin labaran AFP.
TRT Hausa

Rahotanni sun ce kwale-kwalen na tsallaka Kogin Nilu ne tsakanin ƙauyukan Tayba al-Khawad da Deim al-Qarai lokacin da hatsarin ya faru, amma sanarwar gwamnati ba ta bayyana musabbabin lamarin ba.
TRT Hausa

Ganau sun shaida wa AFP cewa kwale-kwalen na ɗauke da kusan mutum 30 a lokacin da ya nutse.
TRT Hausa

Ƙungiyar Sudanese Doctors Network ta bayyana cewa mutane shida daga cikin fasinjojin sun tsira, tana mai alaƙanta hatsarin da raunin sufirin ruwa da kuma rashin kayan tsaro da hanyoyin ceto a farkon faruwar lamarin.
TRT Hausa

Ƙungiyar ta kuma ce da dama daga cikin ‘yan Sudan na dogaro da sufirin ruwa ta amfani da kwale-kwale masu ƙaramin inji, a daidai lokacin da yaƙin cikin gida ke ƙara lalata ababen more rayuwa da hidimomin jama’a a ƙasar.
TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#