Majalisar Dinkin Duniya ta ce hare-haren sun ƙunshi laifukan yaƙi da take haƙƙin bil’adama

Fiye da Mutane 6,000 Sun Mutu a Hare-haren RSF a Darfur

Fiye da mutane 6,000 ne suka rasa rayukansu cikin fiye da kwanaki uku lokacin da rundunar sa-kai ta Rapid Support Forces (RSF) ta ƙaddamar da jerin hare-hare masu tsanani a yankin Darfur na Sudan a ƙarshen watan Oktoba, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.
TRT Hausa

Wani rahoto da ofishin kare haƙƙin bil’adama na MDD ya fitar ya bayyana cewa harin da RSF ta kai domin ƙwace birnin Al Fasher ya ƙunshi munanan ayyuka na zalunci da suka kai matakin laifukan yaƙi.
TRT Hausa

Babban Kwamishinan MDD mai kula da kare haƙƙin ɗan’adam, Volker Türk, ya ce take-haƙƙin da RSF da dakarun haɗin gwiwarsu suka aikata sun nuna yadda rashin hukunta masu laifi ke ƙara tsananta tashin hankali a yankin.
TRT Hausa

Rahoton ya ce RSF da dakarun haɗin gwiwarsu, da aka fi sani da Janjaweed, sun mamaye Al Fasher a ranar 26 ga Oktoba bayan shafe fiye da watanni 18 suna yi wa birnin ƙawanya, lamarin da ya jefa al’ummar yankin cikin mummunan hali.
TRT Hausa

Rahoton MDD mai shafuka 29 ya bayyana jerin munanan laifuka da suka haɗa da kisan kiyashi, fyade, sace mutane domin neman kuɗin fansa, azabtarwa, tsare mutane ba bisa ka’ida ba da kuma ɓacewar mutane, inda a lokuta da dama aka ce hare-haren sun ɗauki salo na kabilanci.
TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#