Umarnin zai fara aiki daga kakar 2026–2027 domin ƙarfafa tattalin arziki

Ghana Ta Umurci Sarrafa Kashi 50 na Koko a Cikin Gida

Gwamnatin Ghana ta ba da umarnin cewa aƙalla kashi 50 cikin 100 na kokon da ake nomawa a ƙasar za a riƙa sarrafa shi a cikin gida daga kakar shekarar 2026 zuwa 2027.
TRT Hausa

Ministan Kuɗin Ghana, Cassiel Ato Forson, ne ya sanar da hakan ranar Alhamis yayin wani taron gaggawa na majalisar zartarwar ƙasar da aka gudanar domin magance matsalolin da ke addabar fannin noman koko.
TRT Hausa

Majalisar zartarwar ta kuma ba da umarnin a farfaɗo da manyan kamfanonin gwamnati biyu da ke da alaƙa da koko, wato kamfanin siyan kayayyaki na ƙasa (PBC) da kamfanin sarrafa koko (CPC), domin su koma aiki nan take.
TRT Hausa

Ministan ya ce za a farfaɗo da kamfanin PBC ne domin ya fara aiki gadan-gadan tare da zama jagora wajen siyan koko ta hanyar lasisi a faɗin ƙasar.
TRT Hausa

Matakin farfaɗo da PBC ya zo ne a daidai lokacin da kamfanonin masu sayen lasisi ke bin kamfanin gwamnati na koko, COCOBOD, bashin kimanin sedi biliyan GH¢2.04, lamarin da ya sa wasu manoma ba su samu an biya su ba tun watan Nuwamban 2025.
TRT Hausa

Majalisar zartarwar ta kuma umurci cewa a ware ragowar kokon kakar 2025–2026 domin a sarrafa shi a cikin gida, a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa sarrafa albarkatu a cikin ƙasa da samar da ayyukan yi a fannin koko.
TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#