Sport
Ziyarar Shugaban Turkiyya Erdogan, wadda aka shirya yi a ranar Talata zuwa Addis Ababa bisa gayyatar Firaiministan Ethiopia Abiy Ahmed, ta zo ne a daidai lokacin da ƙasashen biyu ke tuni da daɗaɗɗiyar dangantaka ta fiye da shekaru 100.
Kafafen yaɗa labarai na cikin gida a Ethiopia sun yi ta yaɗa labarin ziyarar da shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan zai kai ƙasar, inda ake nuna muhimmancinta a fannin diflomasiyya yayin da ƙasashen biyu ke murnar cika shekaru 100 da buɗe ofishin jakadancin Turkiyya a Addis Ababa, babban birnin ƙasar Habasha, wani muhimmin ci-gaba a dangantakar da ta samo asali tun ƙarni na 16.
Kafafen yaɗa labarai na gwamnati da na sauran masu zaman kansu sun bayyana muhimmacin ziyarar, inda suka mayar da hankali kan daɗaɗɗiyar dangantaka da ci-gaban hulɗar tattalin arziki da kuma rawar diflomasiyyar Ankara a yankin.
Ziyarar, wadda aka shirya yi ranar Talata bisa gayyatar Firaminista Abiy Ahmed, za ta zama ta farko da Erdogan zai je Habasha a cikin fiye da shekaru 10.
Kafar watsa labarai ta ƙasar Fana ta bayyana ziyarar a matsayin wani mataki na bunƙasa dangantakar ƙasashen biyu. A wata maƙala da ta wallafa kan Shugaban Turkiyya, kanun labarin ya bayyana shugaban a matsayin "mai gina wani tsari na sabuwar Turkiyya."
Kazalika, a rahoton da kafar yaɗa labarai mai zaman kanta ta Addis Standard ta yi kan ziyarar, ta danganta zuwan shugaban da tashin hankalin da ake fuskanta a yankin Kusurwar Afirka da kuma huldɗar diflomasiyyar Turkiyya ke yi a yankin.
Rahoton ya ce ana sa ran ƙasashen biyu za su sanya hannu kan yarjejeniyoyi na haɗin gwiwa da aka riga aka cim ma a hukumance.
A wani rahoto na daban, Pulse of Africa, wani shafi na kafofin watsa labarai na intanet kan Afrika wanda Shugaba Abiy ya ƙaddamar a watan Oktoban da ya wuce, ya jaddada cewa Turkiyya na ƙarfafa kasancewarta a Bahar Rum da kuma yankin Kusurwar Afirka yayin da Shugaba Erdogan ke ziyara a Addis Ababa don faɗaɗa dangantakar kasuwanci, ababen more rayuwa da tsaro.
A yayin jawabin da ya gabatar a wani taron tuni kan daɗaɗɗiyar dagantakar da ke tsakanin ƙasashen biyu, jakadan Turkiyya a Habasha, Berk Baran, ya ce ziyarar Erdogan ta nuna "ƙaruwar alaƙar da ke tsakanin ƙasashen biyu."
"Turkkiya da Habasha sun jima suna jin daɗin wannan dangantaka mai mahimmanci a fannoni daban-daban, ciki har da dangantakar siyasa, tattalin arziki da zamantakewa," in ji shi.
Dangantakar siyasa mai ɗorewa da tattaunawa
"A cikin yanayin tsarin duniya mai rikitarwa, Turkiyya da Habasha sun gina dangantaka mai ɗorewa ba tare da barin wani na uku ya shiga tsakani ba. Akwai buƙatar a kiyaye tare da ƙarfafa hakan," kamar yadda Emre Yasin Kekec, wani mai bincike da ke zaman kansa daga Turkiyya ya shaida wa Anadolu.
Masu sharhi sun ce dangantakar ta samo asali ne daga fahimta ta siyasa tsakanin juna, duk da cewa muradun ƙasa sun bambanta.
"Ina ganin Turkiyya ta fahimci matsayin Habasha; mun ga hakan a lokacin rikicin Kogin Nilu, haka kuma mun ga hakan a lokacin da take neman hanyoyin shiga teku, kuma wannan ya samo asali ne sakamakon kamanceceniya da ke tsakani na yanayin ƙasa da tarihin ƙasashen biyu," in ji Ibrahim Mulushewa, wani mai bincike kuma shugaban wata ƙungiyar nazarce-nazarce da ke Addis Ababa, yayin da yake magana a wani taron da aka yi domin tunawa da shekaru 100 na dangantakar ƙasashen biyu.
Ya ce wannan kyakkyawar alaƙar ta ba da damar dangantaka ta kai-tsaye tsakanin ƙasashen biyu.
"A wasu lokutan fahimtar Turkiyya ba za ta iya kasance a shafi ɗaya da Habasha ba, amma aƙalla ƙasashen biyu suna ganin alaƙar da ke tsakani, kuma wannan shi ne dalili ya haifar da tattaunawa da kuma hulɗa ta kai-tsaye, wanda hakan ya sa Turkiyya ta yi nasarar shiga tsakani kan batutuwan yanki masu mahimmanci kamar na rikicin Habasha da Somaliya, wanda aka warware ta hanyar sanarwar Ankara mai cike da tarihi," in ji shi.
A jawabinsa a wani taron tattaunawa kan bikin cika shekaru 100 na dangantakar ƙasashen biyu, Baran ya ce "diflomasiyyar da ta shafe shekaru 100 tana da muhimmanci a dangantakar da ke tsakanin Turkiyya da Habasha," yana mai cewa ziyarar Shugaba Erdogan "ta nuna sabon matakin dangantakar ƙasashen biyu."
Masu sharhi sun bayyana cewa, an ci gaba da haɗin gwiwar da aka samu wacce ta ɗore ta hanyar alaƙar zamantakewa da diflomasiyya a hukumance.
‘‘Yawancin tattaunawar suna mai da hankali ne ta fuskantar diflomasiyyar siyasa, yayin da ainihin hulɗar ta zamantakewa ce," in ji Kekec.
Kazalika, masana sun yi nuni kan rawar diflomasiyyar al'adu da ake takawa wajen tsara fahimtar al’umma.
"A mafi yawan lokuta ana watsi da diflomasiyyar al'adu, zamantakewa da na fasaha, inda galibi diflomasiyyar siyasa ce take mamaye sauran fannonin. Ko da yake a ɓangaren Habasha, shirye-shiryen talabijin na Turkiyya da dalibai irina waɗanda suka yi karatu a Turkiyya da kuma al’adun gargajiya sun sa ƙasar ta yi suna mai kyau a faɗin Habasha, a cewar Abdulazizi Dino, malami a jami’ar Addis Ababa wanda ke da digirin digirgir daga jami’ar Ankara.
"A yanayin da duniya ke ci gaba da canzawa, duk da cewa diflomasiyyar gargajiya na taka muhimmiyar rawa, ba za ta yi tasiri sosai ba idan ba haɗa da tallafin ɓangarorin kafafen watsa labarai, da al'adu da kuma zamantakewa ba," in ji shi.
A cewar malaman, ziyarar Erdogan ta nuna wata alama ta wani muhimmin ci gaba na shekaru 100 da kuma ƙoƙarin da ƙasashen biyu ke yi na ƙarfafa alaƙar da ta samo asali daga sanin tarihi, tattaunawar diflomasiyya da kuma ɗaɗaɗɗiyar alaƙar zamantakewa.
Comments
No comments Yet
Comment