Ziyarar na zuwa ne yayin bikin cika shekaru 100 na dangantakar Turkiyya da Habasha

Erdogan Zai Kai Ziyarar Diflomasiyya Ethiopia

Kafafen yaɗa labarai a Ethiopia sun mai da hankali kan ziyarar da shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdoğan zai kai ƙasar, suna bayyana ta a matsayin muhimmin mataki na diflomasiyya yayin da ƙasashen biyu ke murnar cika shekaru 100 da buɗe ofishin jakadancin Turkiyya a Addis Ababa, babban birnin Ethiopia.
TRT Hausa

Ziyarar, wadda aka shirya yi ranar Talata bisa gayyatar Firaministan Ethiopia Abiy Ahmed, za ta zama ta farko da Erdogan zai kai Habasha cikin sama da shekaru goma, tare da mayar da hankali kan bunƙasa hulɗar tattalin arziki da rawar Turkiyya a yankin Kusurwar Afirka.
TRT Hausa

Kafar watsa labarai ta gwamnati, Fana, ta bayyana ziyarar a matsayin wani muhimmin mataki na ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu, yayin da Addis Standard ta danganta zuwan Erdogan da ƙoƙarin Ankara na taka rawa a harkokin tsaro da diflomasiyya a yankin.
TRT Hausa

Rahotanni sun nuna cewa ana sa ran Turkiyya da Ethiopia za su sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyin haɗin gwiwa, musamman a fannonin kasuwanci, ababen more rayuwa da tsaro.
TRT Hausa

Jakadan Turkiyya a Ethiopia, Berk Baran, ya ce ziyarar Erdogan alama ce ta ƙarfuwar alaƙar siyasa, tattalin arziki da zamantakewa tsakanin ƙasashen biyu, inda ya jaddada muhimmancin diflomasiyyar da ta shafe shekaru 100 tana gina wannan dangantaka.
TRT Hausa

Masu sharhi sun bayyana cewa dangantakar Turkiyya da Ethiopia ta ginu ne bisa fahimtar juna ta siyasa da kuma alaƙar zamantakewa, lamarin da ya ba Turkiyya damar shiga tsakani a wasu rikice-rikicen yankin kamar na Ethiopia da Somaliya.
TRT Hausa

Masana sun kuma jaddada rawar diflomasiyyar al’adu, kafafen watsa labarai da mu’amalar jama’a wajen ƙarfafa fahimtar juna, suna cewa ziyarar Erdogan na nuna sabon babi a dangantakar ƙasashen biyu bayan cikar shekaru 100.
TRT Hausa

 
 
 
 
 
#