Operation Hadin Kai ta ce ‘yan ta’adda sun tafka asara bayan farmaki a Pulka da Mandaragirau

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ‘Yan Ta’adda a Borno

Rundunar Sojin Nijeriya ta Operation Hadin Kai (OPHK) ta bayyana cewa dakarunta sun daƙile hare-haren ‘yan ta’adda a arewa maso gabashin Nigeria, inda suka tilasta wa maharan janyewa bayan sun tafka asara mai yawa.
TRT Hausa

A cewar wata sanarwa da kakakin OPHK, Sani Uba, ya fitar, ‘yan ta’adda sun kai hari kan sansanonin soji da ke Pulka da Mandaragirau a ranar 14 ga Fabrairu da nufin ƙwace su, amma dakarun sojin sun tsaya tsayin daka tare da kare matsayinsu.
TRT Hausa

Sanarwar ta ce wasu ‘yan Boko Haram da ISWAP sun fito daga Dajin Sambisa suka kai hari mai ƙarfi a Pulka, sai dai sojoji sun yi musayar wuta na tsawon lokaci tare da daƙile harin.
TRT Hausa

Duk da cewa maharan sun lalata wasu kayayyaki bayan sun kutsa wani ɓangare na katangar sansani, tallafin ƙarin dakaru ya tilasta musu tserewa cikin firgici zuwa dajin Sambisa. Rahotannin sirri sun nuna cewa an kashe wasu ‘yan ta’adda ciki har da wani babban kwamanda mai suna Abou Aisha.
TRT Hausa

A Mandaragirau ma, sojoji sun yi nasarar hana ‘yan ta’adda shiga sansanin, sai dai wasu jami’an tsaro da ‘yan sa kai sun rasa rayukansu yayin kare matsayinsu daga maharan.
TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#