Ma’aikatar Harkokin Waje ta ce ana yaudarar ‘yan ƙasa da alƙawarin aiki kafin tura su fagen yaƙi

Gwamnatin Nijeriya Ta Gargaɗi Jama’a Kan Masu Yaudarar Aiki na Yaƙi a Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta gargaɗi ‘yan ƙasar da su guji faɗawa tarkon masu ɗaukar ma’aikata ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda ke yaudarar jama’a domin tura su shiga yaƙe-yaƙe na makamai a ƙasashen waje.
TRT Hausa

A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta Nijeriya ta fitar a ranar Lahadi a Abuja, gwamnati ta bayyana damuwarta kan ƙaruwar rahotannin yaudarar ‘yan Nijeriya da ɗaukarsu aiki ta hanyoyin da ba su dace ba.
TRT Hausa

Ma’aikatar ta ce ana yi wa mutane alƙawarin ayyuka masu albashi mai tsoka, ayyukan tsaro, damar karatu ko sauƙin samun izinin zama, amma daga bisani a tilasta musu rattaba hannu kan kwantiragin aikin soja tare da tura su wuraren yaƙi.
TRT Hausa

Rahotanni sun nuna cewa masu ɗaukar ma’aikata kan yi amfani da tayin albashi mai yawa, kuɗin shiga aiki da kuma alƙawarin samun zama ɗan ƙasa cikin gaggawa domin jan hankalin jama’a.
TRT Hausa

A wasu lokuta, an ce ana tilasta wa waɗanda abin ya shafa sanya hannu kan takardu a harshen waje ba tare da shawarwarin lauya ba, sannan a ƙwace fasfo dinsu bayan sun isa ƙasar, tare da yiwuwar amfani da bizar yawon buɗe ido ko wasu biza da ba na soja ba.
TRT Hausa

Gwamnatin Tarayya ta jaddada cewa shiga rikice-rikicen makamai a ƙasashen waje ba tare da amincewa ba na iya saɓa wa dokokin Nijeriya da na ƙasa da ƙasa, tare da jefa rayuka cikin haɗari da haifar da manyan matsalolin shari’a.
TRT Hausa

Domin magance matsalar, gwamnati ta ce tana aiki tare da abokan hulɗa na cikin gida da na ƙasa da ƙasa don bincike da wayar da kan jama’a, tare da umartar ofisoshin jakadancin Nijeriya su ƙara sa ido da ba da shawarwari cikin gaggawa.
TRT Hausa

Ma’aikatar ta roƙi iyaye, shugabannin al’umma da cibiyoyin ilimi su wayar da kan matasa, tare da shawarci ‘yan ƙasa su tabbatar da duk wani tayin aiki ko karatu ta hanyoyin hukuma da kuma kai rahoton duk wani abin da ake zargi na zamba ga hukumomin da suka dace.
TRT Hausa

 
 
 
 
 

 

 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#