Murabus ɗin ya zo ne a tsakiyar ce-ce-ku-ce da rikici cikin hukumar

Shugaban NAHCON Ya Ajiye Aiki Gabanin Hajjin 2026

Rahotanni daga Nijeriya na cewa shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya (NAHCON), Sheikh Abdullahi Saleh Pakistan, ya ajiye aikinsa a daidai lokacin da ake shirye-shiryen aikin Hajjin 2026.
TRT Hausa

Har zuwa yanzu ba a bayyana dalilin murabus ɗin ba, sai dai kafofin watsa labaran Nijeriya sun ambato Ahmed Muazu, mai magana da yawun shugaban, yana tabbatar da cewa Sheikh Pakistan ya ajiye mukaminsa.
TRT Hausa

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Sheikh Pakistan a matsayin shugaban NAHCON a shekarar 2024 bayan cire Jalal Arabi, wanda a wancan lokaci aka fara bincike a kansa bisa zargin yin ba daidai ba da kuɗaɗen aikin hajji.
TRT Hausa

A shekarar 2025, Sheikh Pakistan ya jagoranci aikin hajji na farko a matsayinsa na shugaban hukumar, sai dai daga baya shugabancinsa ya fuskanci ce-ce-ku-ce da zarge-zargen badaƙalar kuɗi a aikin hajjin shekarar.
TRT Hausa

Zarge-zargen sun haifar da rikici a cikin hukumar tare da jawo hankalin jama’a, inda aka yi ta musayar yawu kan yadda aka tafiyar da kuɗaɗe da harkokin aikin hajjin.
TRT Hausa

A watan Janairun 2026, rahotanni sun ce wasu kwamishinonin NAHCON sun rubuta takardar ƙorafi zuwa ga Shugaba Tinubu, suna zargin shugaban hukumar da gazawa wajen shugabanci da rashin kyakkyawan tsarin gudanarwa.
TRT Hausa

Rikicin ya tilasta mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima shiga tsakani, inda ya kira taron masu ruwa da tsaki kimanin makonni biyu da suka gabata domin sasanta rikicin da dawo da zaman lafiya a cikin hukumar.
TRT Hausa

 
 
 
 
 
#