Maharan da suka zo kan babura sun kai farmaki kauyuka uku a Borgu

Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30 a Hare-hare a Jihar Neja

‘Yanbindiga ɗauke da makamai sun kashe aƙalla mutane 30 tare da kona gidaje da shaguna a hare-hare da suka kai kan kauyuka uku a Karamar Hukumar Borgu ta Jihar Neja da safiyar ranar Asabar, a cewar mazauna yankin da suka tsira daga harin.
TRT Hausa

Hare-haren, da aka kai kusa da iyakar Jamhuriyar Benin, na daga cikin jerin hare-haren ‘yanbindiga da ke garkuwa da mutane domin neman kudin fansa, lamarin da ke ci gaba da raba al’umma da muhallansu a arewacin Nijeriya.
TRT Hausa

Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Neja, Wasiu Abiodun, ya tabbatar da harin da aka kai a ƙauyen Tunga-Makeri, inda ya ce mutane shida sun rasa rayukansu, an kona gidaje, sannan an sace wasu mutane da har yanzu ba a san adadinsu ba.
TRT Hausa

Wani mazaunin ƙauyen Konkoso, Jeremiah Timothy, ya ce akalla mutane 26 aka kashe a ƙauyensu bayan da maharan suka kai farmaki da sassafe, inda suka harbe-harbe ba kakkautawa tare da kona ofishin ‘yansanda.
TRT Hausa

Timothy ya ƙara da cewa maharan sun shiga Konkoso da misalin ƙarfe 6:00 na safe, yayin da mazauna yankin suka ji jiragen yaƙin soja suna shawagi a sararin samaniya.
TRT Hausa

Wani shaidan gani da ido ya bayyana cewa ‘yanbindigan sun zo ne kan babura sama da 200, inda suka mamaye yankin suna kai hare-hare kan kauyukan da ke kusa.
TRT Hausa

Auwal Ibrahim, wani mazaunin Tunga-Makeri, ya ce maharan sun kai hari ƙauyensu da misalin ƙarfe 3:00 na dare, inda suka harbe-harbe, suka kashe mutane, suka kona shaguna, tare da tilasta wa mazauna kauyen tserewa.
TRT Hausa

Ibrahim ya ce har yanzu jama’a na tsoron komawa gidajensu saboda fargabar cewa ‘yanbindigan na nan a yankin.
TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#