Sport
Dollar
43,5019
0.03 %Euro
51,4277
-0.07 %Gram Gold
6.935,6800
0.38 %Quarter Gold
12.083,1300
0 %Silver
118,9600
0.1 %Harin Ya Faru Kusa da Filin Jirgin Sama na Diori Hamani a Yamai
Reshen ƙungiyar Daesh a yankin Sahel ya bayyana cewa shi ne ya kai harin da aka kai Sansanin Sojin Sama na Nijar da ke kusa da filin jirgin saman ƙasa da ƙasa na Diori Hamani a Yamai, inda ta bayyana hakan ta shafin farfagandarta na Amaq. TRT Hausa
A cikin sanarwar, Daesh ta bayyana harin a matsayin hari na bazata kuma wanda aka shirya, tana mai ikirarin cewa ya haddasa ɓarna mai yawa a sansanin. Kamfanin SITE Intelligence Group, wanda ke bibiyar ayyukan ƙungiyoyin ta’addanci, ya tabbatar da sahihancin wannan ikirari, duk da cewa ƙungiyar ba ta bayyana adadin waɗanda suka mutu ko suka jikkata ba. TRT Hausa
Hukumomin Nijar sun riga sun tabbatar da cewa an kai harin ne daga daren Laraba 28 ga Janairu zuwa safiyar Alhamis 29 ga Janairun 2026, inda Ministan Tsaron Ƙasa ya ce maharan sun kai harin ne a kan babura kusan ƙarfe 12:20 na dare. TRT Hausa
Dakarun Tsaro da Kare Ƙasa na Nijar, tare da taimakon abokan haɗin gwiwarsu na Rasha, sun ɗauki matakin gaggawa tare da fatattakar maharan bayan kusan mintuna talatin na musayar wuta. TRT Hausa
Rundunar sojin ta ce an kashe kimanin maharan 20, ciki har da wanda aka bayyana a matsayin ɗan Faransa, yayin da aka kama mutane 11 da rai, tare da ƙwato makamai, harsasai, babura da kayan aikin soja. TRT Hausa
Sojojin Nijar ba su yi asarar rai ba a harin, sai dai sojoji huɗu sun jikkata, kamar yadda hotunan da aka nuna a gidan talabijin na ƙasa RTN suka tabbatar. TRT Hausa
A lokacin ja da baya, maharan sun harbi jiragen farar-hula uku da ke tsaye a filin jirgin, ciki har da jiragen Asky Airlines biyu da jirgin Air Côte d’Ivoire Airbus A319 guda ɗaya, amma ba a samu asarar rayuka ba. TRT Hausa
Daga cikin ɓarnar da aka samu akwai ƙonewar wata ma’ajiya ta harsasai, lamarin da ya ƙara nuna girman barazanar da harin ya haifar. TRT Hausa
Sansanin Sojin Sama na Base 101 na da matuƙar muhimmanci, kasancewarsa cibiyar haɗin gwiwar dakarun Afirka da Rasha da kuma dakarun Italiya masu aikin tallafi a Nijar, kuma a baya-bayan nan an adana uranium a wurin yayin rikicin da ke tsakanin Nijar da kamfanin nukiliya na Faransa Orano. TRT Hausa
Comments
No comments Yet
Comment