Kasashen biyu na neman rage tashin hankali da farfaɗo da tattaunawa a Gabas ta Tsakiya

Masar da Saudiyya Sun Yi Kira ga Diflomasiyya Tsakanin Amurka da Iran

Ministocin harkokin wajen Masar da Saudiyya sun yi kira da a fifita hanyoyin diflomasiyya tare da ƙirƙirar “yanayi mai kyau” domin sake farfaɗo da tattaunawa tsakanin Amurka da Iran, da nufin cim ma yarjejeniya mai faɗi kuma mai daidaito. TRT Hausa

An bayyana hakan ne a yayin wata ganawa da aka yi a Riyadh tsakanin Ministan Harkokin Wajen Masar, Badr Abdelatty, da Ministan Harkokin Wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan, a ranar Talata, kamar yadda Ma’aikatar Harkokin Wajen Masar ta sanar. TRT Hausa

Ministocin biyu sun kuma tattauna dangantakar kasashensu, inda suka nuna aniyar ƙarfafa haɗin gwiwa da zurfafa daidaiton manufofi tsakanin Masar da Saudiyya. TRT Hausa

Sun jaddada muhimmancin rage tashin hankali a yankin ta hanyar fifita hanyoyin siyasa da diflomasiyya, domin hana barkewar sabon rikici da zai iya jefa yankin cikin rashin daidaito. TRT Hausa

Bangarorin biyu sun bayyana cewa kalubalen tsaro a yankin na buƙatar haɗin kai na ƙasashen Larabawa da ci gaba da tuntuɓa a matsayin ginshiƙi na kare tsaro da zaman lafiyar yankin. TRT Hausa

Game da Gaza, ministocin sun goyi bayan aiwatar da mataki na biyu na shirin Shugaban Amurka Donald Trump, tare da kiran kafa tsarin gudanarwa, tura ƙungiyar kwantar da tarzoma ta ƙasa da ƙasa, da tabbatar da shigar agajin jinƙai ba tare da katsewa ba. TRT Hausa

Sun kuma yi kira da a ƙara ƙoƙarin jinƙai a Sudan domin cim ma tsagaita wuta gabaɗaya da buɗe hanyar tsarin siyasa da ‘yan Sudan za su jagoranta, tare da jaddada muhimmancin kiyaye haɗin kan ƙasar da tsaronta. TRT Hausa


 

 
 
 
 
#