Dollar

43,5051

0.03 %

Euro

51,4363

-0.06 %

Gram Gold

6.932,4600

0.34 %

Quarter Gold

12.083,1300

0 %

Silver

118,7500

-0.07 %

Matakin Na Nuna Ƙara Tsaurara Iko Kusan Shekaru Uku Bayan Juyin Mulki

Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Rusa Dukkan Jam’iyyun Siyasa

Gwamnatin Burkina Faso da sojoji ke jagoranta ta ba da umarnin rusa dukkan jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyi a ranar Alhamis, matakin da ke nuna ƙara tsaurara iko kusan shekaru uku bayan sojoji sun ƙwace mulki a ƙasar. TRT Hausa

Dokar, wadda aka amince da ita a taron majalisar ministoci na mako-mako ƙarƙashin jagorancin shugaban sojoji Ibrahim Traore, ta kuma umarci a mayar da dukkan kadarorin jam’iyyun siyasa da aka rusa zuwa ga gwamnati. TRT Hausa

Hukumomi sun bayyana cewa an tsara dokar ne domin soke tsofaffin dokoki da ke kula da harkokin kuɗi da ayyukan jam’iyyun siyasa a ƙasar, suna mai cewa tsarin ya buƙaci sauyi. TRT Hausa

Ministan Kula da Yankuna, Emile Zerbo, ya ce matakin ya biyo bayan abin da ya kira “cikakkiyar fahimtar” rawar da jam’iyyun siyasa ke takawa wajen haddasa rarrabuwar kai da ɓangaranci a cikin al’umma. TRT Hausa

Zerbo ya bayyana cewa rusa jam’iyyun wani muhimmin ɓangare ne na sake gina ƙasa, yana mai zargin jam’iyyun da kauce wa hurumin da doka ta ba su da kuma taimakawa wajen raba kan ‘yan ƙasa. TRT Hausa

Gwamnati ta ce yawaitar jam’iyyun siyasa ya raunana haɗin kan al’umma, ya lalata shugabanci nagari, kuma ya hana cimma tsaro da kwanciyar hankali. TRT Hausa

A cewar gwamnati, matakin na da nufin kare haɗin kan ƙasa, ƙarfafa haɗin kai a ayyukan gwamnati, da kuma share fagen yin garambawul ga tsarin mulkin siyasa. TRT Hausa

Burkina Faso na ƙarƙashin mulkin soja tun bayan juyin mulkin Satumbar 2022, na biyu cikin shekarar, inda gwamnati ke danganta ɗaukar matakan musamman da matsalar tsaro daga ‘yan ta’adda masu alaƙa da Al-Qaeda da Daesh. TRT Hausa

Tun bayan juyin mulkin, an dakatar da ayyukan jam’iyyun siyasa, sannan aka ɗage zaɓen da aka yi alƙawarin gudanarwa a watan Yulin 2024 har sai abin da hali ya yi, kafin a yanzu a rusa jam’iyyun a hukumance. TRT Hausa



 

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#