Jirgin ya faɗi ne bayan aikin kuɓutar da mara lafiya kusa da Kufra

Hatsarin helikwaftar asibiti ya kashe mutane biyar a Libya

Wani helikwafta na asibiti ya yi hatsari a sansanin Al-Sarra na Libya yayin da yake sauka bayan kammala aikin kuɓutar da mara lafiya, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane biyar, kamar yadda kafafen watsa labaran ƙasar suka ruwaito. TRT Hausa

Rahotanni sun ce hatsarin ya faru ne ranar Litinin, kimanin kilomita 300 daga birnin Kufra a kudu maso gabashin Libya. Daga cikin waɗanda suka mutu akwai mambobin rundunar sufuri ta soji biyu, wani ma’aikacin jinya daga Kufra, da kuma matuƙin jirgin da mataimakinsa waɗanda ‘yan ƙasashen waje ne. TRT Hausa

Kafafen watsa labarai sun bayyana cewa helikwaftar na aikin kuɓutarwa ne bayan wani soja ya jikkata a wani hatsari a yankin hamada, kuma duk da isowar jami’an gaggawa da wuri, babu wanda ya tsira daga cikin waɗanda ke cikin jirgin. TRT Hausa

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#