Binciken ƙasa da ƙasa na ƙara tsananta kan rikicin Sudan

Saudiyya ta yi kira ga RSF ta dakatar da take haƙƙin fararen hula a Darfur

Saudiyya ta yi kira ga dakarun Rapid Support Forces (RSF) da su dakatar da abin da ta kira mummunan take haƙƙin fararen hula, yayin da binciken ƙasa da ƙasa ke ƙara tsananta kan laifukan da ake zargin ana aikatawa a yankin Darfur na Sudan. TRT Hausa

An bayyana kiran ne a daren Litinin a wani zaman tattaunawa a Geneva, bayan jawabin Babban Sakatare na Majalisar Dinkin Duniya kan Hakkokin Bil Adama, Volker Turk, game da tabarbarewar halin da ake ciki a Al Fasher, babban birnin Darfur ta Arewa. TRT Hausa

Volker Turk ya dora alhakin “mugayen laifuka” da aka aikata a Al Fasher kan RSF tare da abokanta da masu tallafa musu, yana mai ambaton hare-hare kan fararen hula da muhimman ababen more rayuwa na jama’a. TRT Hausa

A cikin wata sanarwa da wakilin dindindin na Saudiyya a Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, Jakada Abdulmohsen bin Khothaila ya gabatar, Riyadh ta yi tir da hare-haren RSF kan Al Fasher a watan Oktoban 2025, tare da zargin kai hari kan asibitoci, motocin agaji da wuraren fararen hula. TRT Hausa

Saudiyya ta jaddada bukatar RSF ta bi dokokin jinƙai na ƙasa da ƙasa domin tabbatar da isar da agaji cikin aminci, tare da sake nuna goyon bayanta ga haɗin kan Sudan, tsaro, zaman lafiya da kiyaye halastattun hukumomin gwamnati. TRT Hausa

RSF ta ƙwace ikon Al Fasher a ranar 26 ga Oktoban 2025, kuma tun daga lokacin ƙungiyoyi na cikin gida da na ƙasa da ƙasa ke zarginta da aikata kisan kare dangi a kan fararen hula, yayin da rikici ke ƙara yaɗuwa a jihohin Kordofan. TRT Hausa

Yaƙin da ya ɓarke a Afrilun 2023 tsakanin RSF da sojin Sudan ya jefa ƙasar cikin ɗaya daga cikin mafi munin rikice-rikicen jinƙai a duniya, inda aka kashe dubban mutane tare da tilasta kusan mutum miliyan 13 barin gidajensu. TRT Hausa

 
 
 
 
 
#