Dollar

40,9411

0.09 %

Euro

47,9607

0.44 %

Gram Gold

4.383,8900

0.13 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Hukumar ta ce za a buɗe rajistar masu kaɗa ƙuri’a ta intanet a ranar 18 ga watan Agusta ta hanyar tasharta, cvr.inecnigeria.org.

INEC za ta fara rajistar masu zaɓe a faɗin Nijeriya ranar 18 ga Agustan 2025

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Nijeriya ta ce za a fara gudanar da rajistar masu kaɗa ƙuri’a na shekarar 2025 a duk faɗin ƙasar a ranar 18 ga watan Agusta.

INEC ta bayyana hakan ne a shafinta na X ranar Juma'a.

Hukumar ta ce za a buɗe rajistar masu kaɗa ƙuri’a ta intanet a ranar 18 ga watan Agusta ta hanyar tasharta, cvr.inecnigeria.org.

Ya bayyana cewa za a fara rajistar mutanen nan da mako guda, ranar 25 ga watan Agusta.

A cewarta, za a gudanar da wannan aiki a duk fadin kasar a dukkan ofisoshin kananan hukumomin da kuma wuraren da aka keɓe.

INEC ta ce za a gudanar da aikin ne daga ranar Litinin zuwa Juma'a, daga karfe 9 na safe zuwa karfe 3 na rana.

"Kuri'unku sun ta’allaƙa ne da yin rajistarku. Ka da ku rasa damarku ta yin rajista," in ji shi.

A bisa ƙa’ida ‘yan shekara 18 zuwa sama ne kawai ke da izinin yin zaɓe a Nijeriya.

A shekarar 2027 ne za a sake yin manyan zaɓuka a Nijeriya.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#