Sport
Dollar
40,9411
0.09 %Euro
47,9607
0.44 %Gram Gold
4.383,8900
0.13 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Manyan 'yan siyasa irin su gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da takwaransa na Kaduna Uba Sani da babban abokin hamayyarsa kuma tsohon gwamnan Jihar ta Kaduna Nasir El-Rufai duka sun yi yaƙin neman zaɓe ga 'yan takarar jam'iyyunsu.
A ranar Asabar ɗin nan ne ake gudanar da zaɓukan cike gurbi a wasu mazaɓu da ke sassa daban-daban a faɗin Nijeriya, waɗanda ake gani za su ƙara fito da ƙarfi ko akasin haka na Jam’iyyar APC mai mulki da kuma Jam’iyyun adawa na ƙasar.
Ana gudanar da zaɓukan ne a mazaɓu goma sha shida a jihohi 13 - Adamawa, Anambra, Edo, Enugu, Jigawa, Kaduna, Kano, Kogi, Neja, Ogun, Oyo, Taraba da Zamfara.
Zaɓukan da za a cike gurbinsu sun haɗa da na ‘yan majalisar dattawa da majalisar wakilai da majalisun dokoki na jihohi.
Comments
No comments Yet
Comment