Dollar

40,9411

0.09 %

Euro

47,9607

0.44 %

Gram Gold

4.383,8900

0.13 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Manyan 'yan siyasa irin su gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da takwaransa na Kaduna Uba Sani da babban abokin hamayyarsa kuma tsohon gwamnan Jihar ta Kaduna Nasir El-Rufai duka sun yi yaƙin neman zaɓe ga 'yan takarar jam'iyyunsu.

Ana gudanar da zaɓukan cike gurbi a wasu jihohin Nijeriya

A ranar Asabar ɗin nan ne ake gudanar da zaɓukan cike gurbi a wasu mazaɓu da ke sassa daban-daban a faɗin Nijeriya, waɗanda ake gani za su ƙara fito da ƙarfi ko akasin haka na Jam’iyyar APC mai mulki da kuma Jam’iyyun adawa na ƙasar.

Ana gudanar da zaɓukan ne a mazaɓu goma sha shida a jihohi 13 - Adamawa, Anambra, Edo, Enugu, Jigawa, Kaduna, Kano, Kogi, Neja, Ogun, Oyo, Taraba da Zamfara.

Zaɓukan da za a cike gurbinsu sun haɗa da na ‘yan majalisar dattawa da majalisar wakilai da majalisun dokoki na jihohi.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#