Ana raka ‘yan Nijeriya zuwa iyakar Armenia saboda yaƙin da ke gudana

Nijeriya ta fara kwashe ‘yan ƙasarta daga Iran

Gwamnatin Nijeriya ta fara kwashe ‘yan ƙasarta daga Iran yayin da yaƙin Amurka da Isra’ila da Iran ke ci gaba da tsananta.

Shugabar Hukumar kula da ‘yan Nijeriya da ke ƙasashen waje (NiDCOM), Abike Dabiri-Erewa, ta bayyana cewa jami’an jakadancin Nijeriya a Iran na raka ‘yan ƙasar da ke son barin ƙasar zuwa kan iyakar Armenia domin su samu hanyar tsallaka cikin aminci.

Ta ce jami’an Nijeriya suna jiran ‘yan ƙasar a kan iyakar domin tarbarsu tare da taimaka musu wajen komawa gida.

Dabiri-Erewa ta kuma tabbatar da cewa har zuwa yanzu ba a samu rahoton mutuwar wani ɗan Nijeriya a yaƙin ba.

Sai dai ba ta bayyana adadin ‘yan Nijeriya da ke Iran ko kuma waɗanda aka riga aka kwashe ba.

Rahotanni sun nuna cewa rikicin da ya fara kwanaki 11 da suka gabata ya kashe fiye da mutum 1,300 a Iran, yayin da sama da mutum 12,000 suka jikkata sakamakon hare-haren Amurka da Isra’ila.

Hukumomin Iran sun ce daga cikin waɗanda suka mutu akwai mata da yara, tare da jikkatar ma’aikatan jinya da dama a hare-haren.

Tushen labari: Newstimehub

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#