Sport
Jakadancin Amurka ya shawarci ‘yan ƙasarsa su ƙara tsaurara matakan tsaro
Ofishin jakadancin Amurka a Nijeriya ya yi gargaɗin yiwuwar ‘yan ta’adda su kai hari kan wurare da makarantu masu alaƙa da Amurka a faɗin ƙasar.
A wata sanarwa da ofishin jakadancin ya fitar a Abuja, ya shawarci ‘yan ƙasar Amurka da ke Nijeriya su ɗauki ƙarin matakan tsaro musamman idan za su ziyarci harabar jakadancin Amurka ko makarantu masu alaƙa da ƙasar.
Gargaɗin ya shafi ofisoshin jakadancin Amurka da ke Abuja da Legas, inda aka buƙaci Amurkawa su kasance cikin lura tare da ƙara matakan kariya yayin zuwa waɗannan wurare.
Ofishin jakadancin ya kuma shawarci ‘yan ƙasar su rika sauya hanyoyi da lokutan tafiyarsu domin guje wa yanayin da za a iya hasashen motsinsu.
Haka kuma an buƙace su su kauce wa cunkoson jama’a da zanga-zanga, su sanar da ‘yan uwansu tsare-tsaren tafiyarsu, tare da tabbatar da cewa wayoyinsu na da caji domin amfani cikin gaggawa.
Sanarwar ta kuma shawarci su san hanyoyin fita cikin gaggawa kafin su shiga duk wani gini domin rage haɗarin da ka iya tasowa.
Duk da wannan gargaɗi, ofisoshin jakadancin Amurka a Abuja da Legas za su ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum.
Gargaɗin na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya bayan rikicin da ke tsakanin Amurka da Isra’ila da Iran.
Tushen labari: Newstimehub
Comments
No comments Yet
Nijeriya
Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP a Yobe
- 12 March 2026
- 9 Views
Kotu a Taraba ta daure mutum uku kan safarar makamai
- 12 March 2026
- 7 Views
Nijeriya ta bukaci haɗin kai da ƙasashen Gulf kan mai
- 12 March 2026
- 5 Views
Nijeriya ta fara kwashe ‘yan ƙasarta daga Iran
- 11 March 2026
- 6 Views
Latest News
Mataifa 40 Yapewa Fursa ya Kuingia Uganda Bila Viza
- 12 March 2026
- 9 Views
Farashin Ɗanyen Mai Ya Haura Dala $101 Duk Da Matakin IEA na Fitar da Ganga Miliyan 400
- 12 March 2026
- 8 Views
Afirka ta Kudu Ta Gayyaci Sabon Jakadan Amurka Saboda Kalamansa Kan Manufofin Kabilanci
- 12 March 2026
- 9 Views
Comment