Jakadancin Amurka ya shawarci ‘yan ƙasarsa su ƙara tsaurara matakan tsaro

Amurka ta yi gargaɗin yiwuwar harin ‘yan ta’adda a Nijeriya

Ofishin jakadancin Amurka a Nijeriya ya yi gargaɗin yiwuwar ‘yan ta’adda su kai hari kan wurare da makarantu masu alaƙa da Amurka a faɗin ƙasar.

A wata sanarwa da ofishin jakadancin ya fitar a Abuja, ya shawarci ‘yan ƙasar Amurka da ke Nijeriya su ɗauki ƙarin matakan tsaro musamman idan za su ziyarci harabar jakadancin Amurka ko makarantu masu alaƙa da ƙasar.

Gargaɗin ya shafi ofisoshin jakadancin Amurka da ke Abuja da Legas, inda aka buƙaci Amurkawa su kasance cikin lura tare da ƙara matakan kariya yayin zuwa waɗannan wurare.

Ofishin jakadancin ya kuma shawarci ‘yan ƙasar su rika sauya hanyoyi da lokutan tafiyarsu domin guje wa yanayin da za a iya hasashen motsinsu.

Haka kuma an buƙace su su kauce wa cunkoson jama’a da zanga-zanga, su sanar da ‘yan uwansu tsare-tsaren tafiyarsu, tare da tabbatar da cewa wayoyinsu na da caji domin amfani cikin gaggawa.

Sanarwar ta kuma shawarci su san hanyoyin fita cikin gaggawa kafin su shiga duk wani gini domin rage haɗarin da ka iya tasowa.

Duk da wannan gargaɗi, ofisoshin jakadancin Amurka a Abuja da Legas za su ci gaba da gudanar da ayyukansu na yau da kullum.

Gargaɗin na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya bayan rikicin da ke tsakanin Amurka da Isra’ila da Iran.

Tushen labari: Newstimehub

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#