An kashe fiye da ’yanta’adda 20 yayin artabu a sansanin Goniri

Sojojin Nijeriya sun daƙile harin ISWAP a Yobe

Sojojin Rundunar Haɗin Gwiwa ta Nijeriya ƙarƙashin Operation HADIN KAI sun daƙile wani hari da ake zargin mayakan ISWAP ne suka kai kan sansanin sojoji a Goniri da ke Jihar Yobe.

Rahotanni sun ce harin ya faru ne daga daren Litinin zuwa wayewar garin Talata lokacin da maharan suka yi ƙoƙarin kewaye sansanin sojojin daga ɓangarori da dama.

Majiyoyin tsaro sun bayyana cewa an gano motsin maharan ne ta hanyar na’urorin sa ido yayin da suke tahowa daga ƙauyen Goniri da kuma hanyar Ngamdu junction.

Daga nan sojojin suka mayar da martani tare da tura ƙarin dakarun taimako da jiragen yaƙi domin tallafawa rundunar da ke sansanin.

Jiragen yaƙi na rundunar sama sun kai hare-hare daga sama, lamarin da ya tilasta wa ’yanta’addan janyewa bayan sun yi asara mai yawa.

Rahotanni sun ce fiye da ’yanta’adda 20 ne aka kashe a artabun, ciki har da wani kwamandansu mai suna Abu Yusu.

Bayan daƙile harin, sojojin sun ƙwato makamai da dama da maharan suka bari, ciki har da bindigogin AK-47, bama-bamai na IED da harsasai iri-iri.

Haka kuma sojojin sun gano ƙarin gawarwakin ’yanta’addan a lokacin sintiri da suka yi a yankin Timbuktu Triangle, musamman a Gwaigomari.

Jami’an sojin sun ce wasu daga cikin dakarun Nijeriya sun samu raunuka a yayin artabun amma suna samun kulawar likitoci.

Tushen labari: Newstimehub

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#