Dollar

40,9411

0.09 %

Euro

47,9607

0.44 %

Gram Gold

4.383,8900

0.13 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

A sanarwar da ta fitar a taron, GNSP ta ce ambaliyar ruwa ta rusa gidaje 361.

Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 23 a Jamruriyar Nijar

Rahotanni daga Jamhuriyar Nijar na cewa ambaliyar ruwa ta kashe mutum 23 tare da jikkata 21 yayin da ta raba mutum 42,000 da gidajensu.

Kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ruwaito cewa hukumar kwana-kwana ta ƙasar (GNSP) ce ta bayyana hakan a wani taron maneman labarai da ta gabatar ranar Alhamis.

A sanarwar da ta fitar a taron, GNSP ta ce ambaliya ta rusa gidaje 361. Sai dai ba ta faɗi lokacin da lamarin ya faru ba.

Kazalika GNSP ta tuna wa mutane shawarwarin da ta bayar a baya game da matakan da ya kamata a ɗauka wajen kauce wa hatsarin ambaliyar musamman ƙaurace wa tsallake gadajojin da ruwa ya rufe da kuma barin wuraren ambaliya da kuma rashin zama a gidaje masu rauni. 

Ta kuma gargaɗi mutane game da fakewa ƙarƙshin bishiyoyi da toshe magudanan ruwa da linƙaya a a cikin ƙududdufi da kuma tono bayan ayi ruwa

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#