Sport
Dollar
40,9482
0.01 %Euro
47,6960
-0.17 %Gram Gold
4.393,7100
-0.3 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Gwamnati ta ce rundunonin tsaro sun shiga yankin don dawo da lafiya.
‘Yan bindiga sun kashe akalla mutane 30 a wani hari da suka kai wani masallaci a garin Malumfashi da ke arewa maso yammacin Nijeriya a ranar Talata, a cewar wani mazaunin yankin da kuma wani dan majalisa, abin da ya ƙara adadin wadanda aka kashe daga 13 da aka fara bayarwa.
‘Yan ta’addan sun kai hari ne kan masallacin a garin Unguwar Mantau a yayin da suke Sallar Asuba, inda masu bibiyar rikice-rikice suka bayyana cewa mutum 13 ne suka fara mutuwa.
“An kashe mutane tara a wurin nan take, sannan wasu da dama sun mutu a yinin ranar. Adadin yanzu ya kai 32,” in ji wani mazaunin yankin mai suna Nura Musa a ranar Laraba.
Wani ɗan siyasa na yankin, Aminu Ibrahim, ya shaida wa Majalisar Dokokin Jihar Katsina a ranar Talata cewa mutane 30 aka kashe.
Wani bayani daga Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida da Harkokin Gida na Jihar Katsina, Dr Nasir Muazu, ya ce harin na ramuwa ne saboda nasarar da al’ummar Unguwar Mantau suka samu a kwanaki biyu da suka gabata, inda suka yi wa ‘yan ta’adda kwanton bauna suka kashe da dama daga cikinsu.
Comments
No comments Yet
Comment