MIT ta haɗa manyan wakilai daga Afirka domin tattauna tsaro da haɗin gwiwa

Turkiyya ta shirya Tattaunawar Dabarun Turkiyya da Afirka a Ankara

Cibiyar Leƙen Asiri ta Ƙasa ta Turkiyya (MIT) ta shirya Shirin Tattaunawar Dabarun Turkiyya–Afirka, wanda za a gudanar daga 9 zuwa 10 ga Fabrairu a Ankara, tare da halartar wakilai daga ƙasashen Afirka da dama ciki har da Somalia, Nijeriya, Masar, Sudan da Afirka ta Kudu. TRT Hausa

Shirin na kwanaki biyu ya ƙunshi jawabai da tattaunawa kan tsaro na soja, makamashi da sadarwa, inda Daraktan MIT Academy, Farfesa Talha Kose, ya jaddada muhimmancin Afirka a duniya tare da bayyana cewa Turkiyya na kallon ƙasashen Afirka a matsayin abokan hulɗa na daidaito, ba filin gogayya ko moriyar gajeren lokaci ba. TRT Hausa

Kose ya ce manufofin Turkiyya a Afirka sun ta’allaka ne kan ƙa’idar “Maganin Afirka ga matsalolin Afirka,” wadda ke mayar da hankali kan haɗin gwiwa mai dorewa da mutunta juna. TRT Hausa

A nasa jawabin, Ministan Shari’a na Somalia, Moallim Mahmoud Sheikhali, ya ce dangantakar Afirka da Turkiyya ta kai matakin dabaru da ke buƙatar zurfafa hulɗa, yana mai jaddada cewa alakar ta bambanta da ta tsoffin ƙasashen mulkin mallaka domin an gina ta bisa girmamawa da amfanin juna. TRT Hausa

Sheikhali ya ƙara da cewa Turkiyya ta taka muhimmiyar rawa wajen tallafa wa Somalia a yaƙin da ta’addanci, tsaron teku da magance laifukan da suka ketare iyakoki, yana mai bayyana Turkiyya a matsayin abokin ci gaba da zaman lafiya ga Afirka. TRT Hausa

 
 
 
 
 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#