Uwargidan shugaban Turkiyya da Sarauniyar Jordan sun jaddada ƙarfafa dangantaka
Uwargidan shugaban Turkiyya, Emine Erdoğan, ta gana da Sarauniyar Jordan, Rania Al Abdullah, a ranar Asabar a birnin Istanbul, yayin da Sarauniyar ke rakiyar Sarki Abdullah II a wata ziyarar aiki zuwa Turkiyya. TRT Hausa
Emine Erdoğan ta bayyana cewa ganawar ta kasance mai muhimmanci, inda suka ziyarci wani baje-koli a Fadar Dolmabahçe da ke nuna ayyukan fasaha da al’adun gargajiya na Cibiyoyin Fasahar Hannu na Turkiyya. TRT Hausa
Ta ce tana fatan wannan ganawa za ta ƙara ƙarfafa dangantaka da abota tsakanin Turkiyya da Jordan. TRT Hausa
A gefe guda kuma, Shugaba Recep Tayyip Erdoğan ya gana da Sarki Abdullah II, inda suka tattauna kan ƙarfafa dangantaka, zaman lafiya da tsaro a yankin Gabas ta Tsakiya. TRT Hausa
Bayan ganawar, an ba Shugaba Erdoğan lambar girmamawa ta Order of al-Hussein bin Ali, mafi girma daga cikin lambobin girmamawa na Masarautar Jordan, a matsayin yabo ga rawar da yake takawa wajen ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu. TRT Hausa
Sarki Abdullah ya bayyana cewa ganawar da Shugaba Erdoğan ta kasance mai amfani sosai, kuma ta buɗe sabon babi na haɗin gwiwa tsakanin Turkiyya da Jordan a fannoni da dama ciki har da kasuwanci, ilimi, sufuri da tsaro. TRT Hausa