Ziyarar Janar Tiani na nuna sassaukar dangantaka bayan watanni na rashin jituwa

Shugaban Nijar Ya Kai Ziyarar Aiki Aljeriya

Shugaban Nijar Abdourahamane Tiani ya isa Aljeriya ranar Lahadi domin wata ziyara ta aiki, inda ya gana da Shugaba Abdelmadjid Tebboune, a abin da ake ganin na nuni da kawo ƙarshen fiye da watanni 10 na rashin jituwa tsakanin ƙasashen biyu.
TRT Hausa

Fadar shugaban ƙasar Aljeriya ta bayyana cewa Tebboune ya karɓi Tiani, wanda ke jagorantar wata babbar tawaga, kamar yadda sanarwa ta gajeru da aka wallafa a shafin Facebook na fadar shugaban ƙasar ta nuna, ba tare da ƙarin bayani ba.
TRT Hausa

Gidan talbijin na ƙasar Aljeriya ya ruwaito cewa Tebboune ya tarbi takwaransa na Nijar a filin jirgin sama na Houari Boumediene International Airport a Algiers, inda aka shirya bikin maraba na musamman da faretin ban-girma da daga tutocin ƙasashen biyu.
TRT Hausa

Manyan jami’an Aljeriya sun halarci taron, ciki har da kakakin majalisar dokoki Azzouz Nasri, Hafsan soji Janar Said Chanegriha, Ministan Harkokin Waje Ahmed Attaf, da Ministan Ma’adinai Mohamed Arkab, kamar yadda talbijin na ƙasa ya bayyana.
TRT Hausa

Bayan haka, Tebboune da Tiani sun yi tattaunawa a wani ɓangare na musamman a filin jirgin saman tare da mambobin tawagoginsu, sai dai ba a bayyana cikakken bayani kan abin da suka tattauna ko tsawon ziyarar ba.
TRT Hausa

Kafofin watsa labarai da masu sharhi sun ce irin wannan tarba da kuma ganawar manyan jami’ai na nuni da yunƙurin kawo ƙarshen tsamin dangantaka da ta ɗauki fiye da watanni 10.
TRT Hausa

A ranar Alhamis, Aljeriya ta sanar da komawar jakadanta a Nijar Ahmed Saadi, matakin da ya biyo bayan komawar jakadan Nijar a Aljeriya Aminou Malam Manzo, lamarin da ya nuna farfaɗowar alaƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu.
TRT Hausa

Rikicin diflomasiyyar ya fara ne tun watan Afrilu bayan Nijar, Burkina Faso da Mali, mambobin ƙawancen AES, sun janye jakadunsu daga Aljeriya sakamakon zargin kakkaɓo jirgin Mali maras matuƙi, zargi da Aljeriya ta musanta.
TRT Hausa

Aljeriya da Nijar na da iyaka mai tsawon kusan kilomita 950, kuma suna haɗa kai a manyan ayyukan yanki ciki har da titin hamadar Sahara da shirin bututun gas da zai kai iskar gas daga Nigeria zuwa Turai ta Nijar da Aljeriya.
TRT Hausa

 
 
 
 
 

 

 

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#