Sport
- Sport
- World
- Insight
- Africa
- Business
- Life
- Opinion
- Staff Reporter
- Business & Technology
- Pauline Odhiambo
- Politics
- Charles Mgbolu
- Arts & Culture
- War On Gaza
- Business & Technology
- Guinness World Record For The Longest Chess
- Cryptocurrency Trading Platform
- Arts & Culture
- Sylvia Chebet
- The Record Attempt Kicked Off On April 17th
- Despite Efforts To Stop The Killings.
- Emmanuel Oduor
- Climate Change
- Semblance Of Security Returns
- Medicinal Plants
- Firmain Eric Mbadinga
- Kategori bulunamadı
- Nuri Aden
- Burna Boy Has Worked To Carve A Unique Space For Himself
- Dayo Yussuf
- Edward Qorro
- Sudan Begins Rebuild Of Khartoum Amid Devastating Civil War
- Chess Federation
- Millicent Akeyo
- From Onana To Kudus: African Stars Missing At Afcon
- Egypt Recorded 19 Million Tourists In 2025: Minister
- Brian Okoth
- Died At The Age Of 54
Ziyarar Janar Tiani na nuna sassaukar dangantaka bayan watanni na rashin jituwa
Shugaban Nijar Abdourahamane Tiani ya isa Aljeriya ranar Lahadi domin wata ziyara ta aiki, inda ya gana da Shugaba Abdelmadjid Tebboune, a abin da ake ganin na nuni da kawo ƙarshen fiye da watanni 10 na rashin jituwa tsakanin ƙasashen biyu.
TRT Hausa
Fadar shugaban ƙasar Aljeriya ta bayyana cewa Tebboune ya karɓi Tiani, wanda ke jagorantar wata babbar tawaga, kamar yadda sanarwa ta gajeru da aka wallafa a shafin Facebook na fadar shugaban ƙasar ta nuna, ba tare da ƙarin bayani ba.
TRT Hausa
Gidan talbijin na ƙasar Aljeriya ya ruwaito cewa Tebboune ya tarbi takwaransa na Nijar a filin jirgin sama na Houari Boumediene International Airport a Algiers, inda aka shirya bikin maraba na musamman da faretin ban-girma da daga tutocin ƙasashen biyu.
TRT Hausa
Manyan jami’an Aljeriya sun halarci taron, ciki har da kakakin majalisar dokoki Azzouz Nasri, Hafsan soji Janar Said Chanegriha, Ministan Harkokin Waje Ahmed Attaf, da Ministan Ma’adinai Mohamed Arkab, kamar yadda talbijin na ƙasa ya bayyana.
TRT Hausa
Bayan haka, Tebboune da Tiani sun yi tattaunawa a wani ɓangare na musamman a filin jirgin saman tare da mambobin tawagoginsu, sai dai ba a bayyana cikakken bayani kan abin da suka tattauna ko tsawon ziyarar ba.
TRT Hausa
Kafofin watsa labarai da masu sharhi sun ce irin wannan tarba da kuma ganawar manyan jami’ai na nuni da yunƙurin kawo ƙarshen tsamin dangantaka da ta ɗauki fiye da watanni 10.
TRT Hausa
A ranar Alhamis, Aljeriya ta sanar da komawar jakadanta a Nijar Ahmed Saadi, matakin da ya biyo bayan komawar jakadan Nijar a Aljeriya Aminou Malam Manzo, lamarin da ya nuna farfaɗowar alaƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu.
TRT Hausa
Rikicin diflomasiyyar ya fara ne tun watan Afrilu bayan Nijar, Burkina Faso da Mali, mambobin ƙawancen AES, sun janye jakadunsu daga Aljeriya sakamakon zargin kakkaɓo jirgin Mali maras matuƙi, zargi da Aljeriya ta musanta.
TRT Hausa
Aljeriya da Nijar na da iyaka mai tsawon kusan kilomita 950, kuma suna haɗa kai a manyan ayyukan yanki ciki har da titin hamadar Sahara da shirin bututun gas da zai kai iskar gas daga Nigeria zuwa Turai ta Nijar da Aljeriya.
TRT Hausa


Comments
No comments Yet
Siyasa
Martanin duniya a yayin da Isra’ila ke rajistar mallake Gabar Yammacin Kogin Jordan
- 17 February 2026
- 9 Views
Majalisar Dattawa ta amince da aikawa da sakamakon zaɓe ta intanet
- 11 February 2026
- 21 Views
An kira jakadan Ghana a Nijeriya gida kan zargin maguɗin zaɓe
- 10 February 2026
- 16 Views
Masar da Saudiyya Sun Yi Kira ga Diflomasiyya Tsakanin Amurka da Iran
- 04 February 2026
- 25 Views
Latest News
Morocco residents return to sacked city after floods recede
- 17 February 2026
- 3 Views
Türkiye's enduring footprints in Africa: A story of partnership and hope
- 17 February 2026
- 6 Views
Sojojin Amurka sun isa arewa maso gabashin Nijeriya
- 17 February 2026
- 8 Views
Martanin duniya a yayin da Isra’ila ke rajistar mallake Gabar Yammacin Kogin Jordan
- 17 February 2026
- 9 Views
Comment