Ziyarar na da nufin ƙarfafa alaƙa da faɗaɗa haɗin kai tsakanin Nijeriya da Turkiyya

Shugaba Tinubu Zai Kai Ziyarar Aiki Turkiyya

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu zai tashi daga Abuja ranar Litinin, 26 ga Janairun 2026 zuwa Ankara, babban birnin Turkiyya, domin kai ziyarar aiki da ta shafi ƙarfafa alaƙar diflomasiyya da faɗaɗa haɗin kai a fannoni daban-daban tsakanin ƙasashen biyu. (TRT Hausa)

A cewar sanarwar da mai magana da yawun shugaban Nijeriya, Bayo Onanuga, ya fitar, ziyarar za ta mayar da hankali ne kan bunƙasa haɗin kai a fannonin tsaro, ilimi, walwala, ƙirƙire-ƙirƙire da kuma sufurin jiragen sama. (TRT Hausa)

Sanarwar ta ce yayin ziyarar, Nijeriya da Turkiyya za su tattauna kan harkokin siyasa, diflomasiyya, kuɗi, sadarwa, cinikayya da zuba jari, tare da shirye-shiryen sanya hannu kan yarjejeniyoyi masu muhimmanci. (TRT Hausa)

Kazalika, manyan jami’ai da ‘yan kasuwa daga ɓangarorin biyu za su gudanar da taruka tare da rattaba hannu kan yarjejeniyoyi a fannoni kamar binciken kimiyya, makamashi, fasaha, watsa labarai, sadarwa da haɗin kai a fannin soji. (TRT Hausa)

Tawagar Shugaba Tinubu ta ƙunshi manyan jami’an gwamnati da suka haɗa da Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Tuggar; Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (ritaya); da Mai Bai wa shugaban ƙasa shawara kan sha’anin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, tare da wasu manyan jami’ai. (TRT Hausa)

 
 
 
 
 
#