Dollar

41,4171

0.21 %

Euro

48,7056

-0.32 %

Gram Gold

4.902,8900

1.34 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Faɗuwar ta faru ne sakamakon ruwan sama mai yawa da iska mai karfi, inda kuma ayyukan masu lalata turakun suka bayar da gudunmawa, inda aka gano cewa an cire muhimman sassan turken.

Sassa daban-daban na Jihar Kaduna na cikin duhu sakamakon faɗuwar turken dakon lantarki

Sassa daban-daban na Jihar Kaduna da ke arewacin Nijeriya na cikin duhu sakamakon faɗuwar wani turken da ke dakon lantarki, kamar yadda kamfanin da ke dakon wutar lantarki na Nijeriya TCN ya tabbatar.

Mai magana da yawun TCN, Ndidi Mbah, ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a turke mai lamba 7 da ke kai wa Kaduna wuta a yankin Rigasa na Karamar Hukumar Igabi.

Faɗuwar ta faru ne sakamakon ruwan sama mai yawa da iska mai karfi, inda kuma ayyukan masu lalata turakun suka bayar da gudunmawa, inda aka gano cewa an cire muhimman sassan turken.

Sakamakon haka, sassa daban-daban musamman na kudancin jihar sun rasa lantarki, inda lamarin ya shafi gidajen jama’a da masana’antu.

“Faɗuwar turken ya jawo katsewar wutar lantarki zuwa wasu cibiyoyin rarraba wutar lantarki na Kaduna Electric, musamman waɗanda ke bayar da wuta ga Kudancin Kaduna,” in ji sanarwar.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#