Dollar

41,4171

0.21 %

Euro

48,7056

-0.32 %

Gram Gold

4.902,8900

1.34 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

“Ni ba wawa ba ne. Da a ce ina son wa’adi na uku, na san yadda zan yi na nema. Kuma babu wani ɗan Nijeriya, mai rai ko matacce, da zai ce na kira shi na gaya masa ina son wa’adi na uku,” in ji tsohon shugaban ƙasar.

Obasanjo ya musanta neman wa’adi na uku, ya ce da ya ga dama da ya samu

Tsohon Shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya karyata zargin da aka jima ana yi masa kan cewa ya taɓa neman tsawaita wa’adin mulkinsa, inda ya jaddada cewa bai taɓa neman wa’adi na uku ba.

Ya bayyana haka ne a yayin wani taro na Democracy Dialogue da Gidauniyar Goodluck Jonathan ta shirya a Accra, Ghana.

Obasanjon ya ce babu wani ɗan Nijeriya, mai rai ko matacce, da zai iya cewa gaskata cewa ya taɓa roƙon goyon baya domin neman wa’adi na uku.

“Ni ba wawa ba ne. Da a ce ina son wa’adi na uku, na san yadda zan yi na nema. Kuma babu wani ɗan Nijeriya, mai rai ko matacce, da zai ce na kira shi na gaya masa ina son wa’adi na uku,” in ji tsohon shugaban ƙasar.

Obasanjo ya jaddada cewa a zamanin mulkinsa ya nuna ƙwarewarsa wajen cim ma manufofin ƙasa da ke da wuyar cimmawa, inda ya kawo misalin yadda Nijeriya ta samu afuwar bashi a lokacin mulkinsa a matsayin babban ƙalubale fiye da neman wa’adi na uku.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#