Sport
Dollar
41,3875
0.23 %Euro
48,6879
-0.27 %Gram Gold
4.900,0000
1.28 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Kwamishinan ya kuma ce gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wani jami’in da aka samu da laifi.
Gwamnatin jihar Sokoto ta dakatar da wasu shugabannin makarantu shida bisa zargin rashin bin doka da kuma karbar kudade ba tare da izini ba dangane da sakamakon jarabawar karamar sakandare (JSS).
Kwamishian Ilimi a matakin farko da na sakandare na jihar, Ahmad Ila ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na Ma’aikatar Ilimi, Ibrahim Iya ya fitar, kamar yadda gidan talabijin na Channels ya rawaito.
“Ba a yarda wani shugaban makaranta ya yi wani abu da ya saɓa wa doka ko tatsar ɗalibai da iyayensu ba,” in ji Kwamishina Ila.
Ya kara da cewa "Dole ne a tafiyar da makarantunmu ta hanyar da ta dace, ba da son rai ba."
Kwamishinan ya kuma ce gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wani jami’in da aka samu da laifi.
Shugabannin da abin ya shafa sun fito ne daga Makarantar Sakandaren ’Yan Mata ta Nana, da Makarantar Sakandare ta Gwamnati (GDSS) Gagi da GDSS Mana da Giginya Memorial College da Mana Basic Secondary School da kuma GDSS Silame.
Comments
No comments Yet
Comment