Dollar

41,4171

0.21 %

Euro

48,7056

-0.32 %

Gram Gold

4.902,8900

1.34 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

A yayin taron, ta gana da Sheikha Moza bint Nasser, mahaifiyar Sarkin Qatar, Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani.

Matar Shugaban Turkiyya ta yi kira da a yi gaggawar ɗaukar matakin dakatar da 'kashe ilimi' a Gaza

Matar Shugaban Kasar Turkiyya, Emine Erdogan ta sanya hannu kan wata sanarwa ta hadin gwiwa domin hana yara a Gaza rasa damarsu ta samun ilimi sakamakon kisan kiyashin da Isra'ila ke yi a yankin Falasdinawa.

Emine Erdogan ta raka Shugaban Kasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan zuwa Taron Kolin Hadin Kan Kasashen Musulmi da Kungiyar Kasashen Larabawa wanda aka gudanar a Doha, babban birnin Qatar, a ranar 15 ga Satumba.

A yayin taron, ta gana da Sheikha Moza bint Nasser, mahaifiyar Sarkin Qatar, Sheikh Tamim bin Hamad Al Thani.

Bayan taron, gidauniyar Education Above All Foundation, wacce Nasser ta kafa, ta shirya wata sanarwa ta hadin gwiwa mai taken “Shekara mai tsanani ga ilimin yara da ke rayuwa a yankunan rikici.”

Sanarwar ta yi kira da a dauki matakan gaggawa domin kawo karshen cin zarafin da ake yi wa yara da tsarin ilimi a wuraren da ke fama da rikici, musamman a Gaza.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#