Dollar

41,0483

0 %

Euro

47,8442

0.02 %

Gram Gold

4.474,1900

-0.09 %

Quarter Gold

0,0000

%

Silver

0,0000

%

Zuwa lokacin wallafa wannan labari dai hukumar kula da layukan dogo ta Nijeriya ba ta ce komai a kan lamarin ba, sannan ba a san musabbabin faruwar hatsarin ba.

Jirgin ƙasan Kaduna-Abuja na Nijeriya ya yi hatsari bayan sauka daga layinsa

Jirgin ƙasan da ke zirga-zriga tsakanin Abuja zuwa Kaduna a Nijeriya ya yi hatsari bayan da ya sauka daga layinsa a ranar Talata.

Lamarin ya faru ne a garin Asham, kamar yadda wani mai amfani da shafin Facebook, Imo Onyekwere ya fara wallafa faruwar lamarin kai-tsaye ta bidiyo a shafinsa.

Hatsarin ya faru da misalin ƙarfe 11 na safe, jim kaɗan bayan tashin jirgin daga Abuja zuwa Kaduna.

A cikin bidiyon, ana iya ganin yadda taragun jirgin suka tuntsura, kuma mutane sun taru a wajen suna kallon abin da ya faru da ƙoƙarin aikin ceto, yayin da wasu da suka fi kama da fasinjoji na tsaye cirko-cirko.

Hukumar kula da layukan dogo ta Nijeriya, NRC ta ce tuni an tura tawagogin agaji da na jami'an lafiya don kai waɗanda suka jikkata asibiti.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#