Sport
Dollar
41,0483
0 %Euro
47,8610
0.02 %Gram Gold
4.474,4200
-0.09 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%Gwamna Bala Mohammed ya ce ‘yan Nijeriya ne suke kira ga tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya dawo mulki, ba Jam’iyyar PDP kawai ba.
Gwamna Jihar Bauchi da ke Nijeriya, Bala Mohammed, ya bayyana dalilin da ya sa Jam’iyyar adawa ta PDP ta miƙa wa yankin kudancin ƙasar takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Yayin da yake zanta wa da TRT Afrika Hausa, gwamnan wanda shi ne shugaban ƙungiyar gwamnoni na Jam’iyyar ta PDP, ya ce jam’iyar ta ɗauki wannan matakin ne domin kauce wa irin kuskuren da ta yi a baya wanda ya kawo mata rarrabuwar kai.
A zaɓen 2023 dai, toshon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ne ya tsaya takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar, bayan shekara takwas da marigayi Shugaban Muhammadu Buhari ya yi yana mulkin ƙasar.
Ƙin yarda ɗan arewa ya sake mulki bayan mulkin Buhari ya sa wasu daga cikin ’yan jam’iyyar PDP suka mara wa ɗan takarar jam’iyyar APC Bola Tinubu, wanda ya fito daga kudu, baya.
Rarrabuwar kai
“Haka kuma maganar shugabanci tunda yanzu mun yi la’akari cewa akwai bambance-bambance akwai rarrabuwar kai a wannan tsagi na Arewa da Kudu, don haka ya kamata mu ma mu samu shugaban ƙasa wanda zai fito daga kudu,” in ji Gwamna Bala Mohammed.
“Idan ma za a fafata a zaɓe ne, to a yi zaɓe tsakanin ɗan kudu da ɗan kudu. Mu ma mu ba su dama su yi shekara takwas. Kar mu yi irin wancan kuskuren da muka yi wanda ya kawo mana rarrabuwar kai. Mai girma Atiku Abubakar ya karɓa alhali mutanen kudu suna ganin cewa su ya kamata su yi,” kamar yadda gwmanan ya shaida wa TRT Afrika Hausa.
Da aka tambaye shi ko wannan na nuna cewa wasu daga cikin ‘yan jam’iyyar ne ke bibiyar tsohon shugaban ƙasar Nijeriya Goodluck Jonathan ya sake tsayawa takara, sai ya ce ba haka lamarin yake ba, amma tsohon shugaban ƙasar na da ‘yancin sake yin takara.
Comments
No comments Yet
Comment