Iran ta sanar da sabon tsarin jagoranci da zaman makoki na kwanaki 40

An nada Alireza Arafi jagoran wucin-gadi bayan mutuwar Khamenei

An nada Alireza Arafi a matsayin mamba a Majalisar Jagoranci ta Iran kuma wanda zai jagoranci majalisar na wucin-gadi kafin a naɗa wanda zai gaji Ali Khamenei, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na ISNA ya ruwaito.

Arafi, malamin addini kuma mamba a Majalisar Shura ta Iran, zai yi aiki tare da Shugaba Masoud Pezeshkian da Babban Alkali Gholamhossein Mohseni Ejei a cikin Kwamitin Jagoranci na wucin-gadi.

Rahotanni sun ce an kashe Khamenei a hare-haren da Isra'ila da Amurka suka kai, lamarin da ya sa Sojojin Juyin Juya Hali na Iran suka yi alƙawarin ɗaukar fansa.

Gidan talabijin na gwamnati ya sanar da zaman makoki na kwanaki 40 da kuma hutu na kwanaki bakwai ga jama'a bayan mutuwar jagoran mai shekaru 86, wanda ya riƙe madafun iko tun 1989.

An kuma ruwaito cewa an kashe wasu manyan jami'ai da kuma wasu 'yan uwansa a hare-haren da aka kai, yayin da wasu majiyoyi suka ce an kai harin ne a lokacin da yake ganawa da manyan mataimakansa a wani wuri mai tsaro.

Tushen labari: TRT Hausa

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#