Ƙasashe a yankin dole su samar da mafita ga matsalolin yankin, a cewar Erdogan yayin taron manema labarai tare da Firayiministan Ethiopia Abiy a Addis Ababa.

Erdogan: Amincewar da Isra'ila ta yi wa Somaliland ba zai amfani kowa ba

Shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan a ranar Talata ya taɓo batun matakin Isra’ila na amincewa da Somaliland a matsayin ƙasa mai ’yanci da ikon gudanar da kanta, kuma ta kasance ƙasa ɗaya tilo da ta yi hakan, yana mai jaddada cewa wannan mataki ba zai amfani Somaliya ko yankin ba.

“Ina so in sake jaddada cewa amincewar Isra’ila da Somaliland ba zai amfani Somaliland ko Yankin Kusurwar Afirka ba,” in ji Erdogan a wata tattaunawa da manema labarai tare da Firayiministan Ethiopia Abiy Ahmed a Addis Ababa.

Ankara na ganin cewa ya kamata kasashen yankin su samar da mafita ga matsalolin yankin, in ji Erdogan, yana kira ga ƙasashen Kusurwar Afirka da kada su bari a mayar da shi “fagen fafatawar ƙasashen waje.”

Yana mai jaddada dangantakar diflomasiyya tsakanin Turkiyya da Habasha, Erdogan ya ce abin alfahari ne cewa fiye da kamfanonin Turkiyya 200, da jarin da ya kai $2.5 biliyan, suna tallafa wa samar da ayyukan yi ga kusan mutane 20,000 a Habasha.

‘Neman damar zuwa teku’

A ɗaya hannun, Firiyiministan Habasha ya ce ya nemi goyon bayan Turkiyya wajen ƙoƙarin Addis Ababa na tabbatar da samun damar zuwa teku, yana bayyana wannan a matsayin batu mafi muhimmanci a tattaunawarsa da shugaban Turkiyya.

Abiy ya faɗa a taron na manema labarai cewa ya tattauna buƙatar Habasha ta samun “damar zuwa teku” tare da Shugaban Turkiyya, kuma ya yi maraba da irin tattaunawa mai ƙarfi da ma’ana kan wannan batu.

Habasha, wadda ta kasance ƙasa ba ta da teku tun bayan samun ’yancin Eritrea a 1993, ta taɓa bayyana samun tabbacin hanyar teku a matsayin muhimmin abin da ya shafi dabarun ƙasa.

Ziyarar Erdogan ta kasance ɗaya daga cikin muhimman ziyarori da ba a fiye ganin irin su ba da suka ƙunshi ministocin harkokin waje da tsaro na Türkiye, da sauransu, kuma ta zo ne yayin da ƙasashen biyu ke ƙoƙarin ƙarfafa dangantakar tattalin arziki da siyasa a lokacin da ake cikka shekaru 100 da alaƙa tsakanin ƙasashen wadda ta fara a 1926.

Shugabannin sun tattauna faɗaɗa huldar kasuwanci, inda jami’an Habasha suka ce dukkan ɓangarorin suna son ƙara ciniki tsakaninsu zuwa akalla $1 biliyan.

Abiy ya kuma ƙarfafa gwiwar ƙarin masu zuba jari na kamfanonin Turkiyya a Habasha, wadda tuni ke ɗauke da ɗaya daga cikin mafi yawan tarin kamfanonin Turkiyya a Afirka kudu da hamadar Sahara, musamman a masana’antu da gine‑gine.

Bangarorin biyu sun kuma tattauna haɗin gwiwa a matakin duniya, ciki har da tattaunawar sauyin yanayi da suka shafi COP31, wanda za a gudanar a Turkiyya a shekara mai zuwa, sannan a Ethiopia.

Comments

Comment

Comment Your email address will not be published. Required fields are marked*

No comments Yet

#