Sport
Dollar
39,1627
0.01 %Euro
44,7129
0.31 %Gram Gold
4.217,2200
-0.11 %Quarter Gold
0,0000
%Silver
0,0000
%A ranar Lahadi, maharan sun kashe mutane 14 a garin Ankpali, sannan kuma a daren Lahadi a ƙauyen Naka na Ƙaramar Hukumar Gwer West, mutane 11 aka kashe, kamar yadda hukumomi suka tabbatar.
Wasu 'yan bindiga sun kashe aƙalla mutum 25 a hare-hare guda biyu da suka kai a Jihar Benue da ke tsakiyar arewacin Nijeriya, kamar yadda mahukunta na cikin gida suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Litinin.
Wannan shi ne hari na baya-bayan nan a yankin wanda ya yi ƙaurin suna wurin samun rikice-rikice musamman tsakanin manoma da makiyaya.
A ranar Lahadi, maharan sun kashe mutane 14 a garin Ankpali, in ji Adam Ochega, shugaban karamar hukumar Apa, yana mai gargaɗin cewa "har yanzu akwai barazana a wasu wurare."
Makiyaya sun jima suna rikici da manoma a Benue kan samun damar amfani da filaye da albarkatu.
A wani rahoto na baya-bayan nan, Amnesty International ta bayyana cewa mutane 6,896 aka kashe a cikin shekaru biyu da suka gabata a Benue, wanda yanki ne na Nijeriya mai addinai daban-daban, inda irin waɗannan rikice-rikicen ke ɗaukar wani salo na ƙabilanci.
Yawan kai hare-hare
Kakakin 'yan sanda ta tabbatar da harin amma ba ta bayar da adadin waɗanda suka mutu ba.
A wani hari makamancin haka da ya faru a daren Lahadi a ƙauyen Naka na Ƙaramar Hukumar Gwer West, mutane 11 aka kashe.
"Zuwa yanzu mun gano gawawwaki 11 kuma mutane biyar sun samu raunuka," in ji shugaban Ƙaramar Hukumar Gwer West, Ormin Victor a tattaunawarsa da AFP.
A watan da ya gabata, mutane 44 aka kashe a cikin kwanaki huɗu a Gwer West.
Ba a bayyana dalilan tashin hankalin a wannan harin ba, amma Victor ya ɗora alhakin "hare-haren da aka kai kan makiyaya Fulani. Makiyayan ba su yi tsokaci kan zargin ba.
Gasa kan filaye
Sai dai, makiyayan suna yawan cewa su ma suna fuskantar hare-hare daga manoma da ƙwace filaye da kuma sa wa dabbobinsu guba.
Filayen da manoma da makiyaya ke amfani da su a tsakiyar Nijeriya na kara shiga matsin lamba daga sauyin yanayi da kuma ƙaruwar yawan jama'a, wanda ke haifar da gasa mai tsanani kan filaye masu iyaka.
Jihar Benue na ɗaya daga cikin jihohin da rikice-rikicen tsakanin makiyaya da manoma suka fi shafa, inda manoma ke zargin makiyaya da lalata gonakinsu ta hanyar kiwon shanu. Wannan ya haifar da jerin hare-hare na ramuwar gayya tsakanin bangarorin biyu.
A watan Afrilu kadai, hare-hare a fadin jihar Benue da makwabciyarta Filato sun yi sanadin mutuwar fiye da mutum 150.
Comments
No comments Yet
Comment